LEADERSHIP A Yau 20 Ga Afrilu 2018

Page 1

20.04.18

AyAU JUMA'A LEADERSHIP Don Allah Da Kishin Qasa

www.leadershipayau.com Leadership A Yau

JARIDAR HAUSA

LeadershipAyau

20 Ga Afrilun 2018 (3 Ga Sha’aban, 1439)

TA FARKO MAI FITOWA KULLUM A NIJERIYA

Bugu na: 032

N150

PDP Na Shirin Yin Maja Da Sauran Jam’iyyu? Daga Abdulrazaq Yahuza Jere, Abuja

Shugaban babbar jam’iyyar adawa a Nijeriya ta PDP, Prince Uche Secondus ya bayyana cewa jam’iyyar tana tattaunawa da sauran jam’iyyun adawa, da qungiyoyi masu zaman kansu, da tsofaffin shugabanni na qasa gabannin zaven 2019.

Da yake jawabi a lokacin taron gaggawa na kwamitin gudanarwar jam’iyyar a Abuja jiya Alhamis, shugaban na PDP ya ce maqasudin faxaxa tuntuvar tasu shi ne haxa qarfi da qarfe domin kafa sabuwar gwamnati a 2019 don “ceto Nijeriya”. Sai dai kuma shugaban bai yi cikakken bayani kan jam’iyyar maja take son yi da sauran jam’iyyu ba, illa kafe kai da fata

da ya yi cewa dole ne su kori APC daga karagar mulki saboda ta gaza biya wa ‘Yan Nijeriya buqatunsu. “Wannan mummunan koma-bayan da qasar ta faxa ciki babban qalubale ne a gare mu a matsayin babbar jam’iyyar adawa mu sauya salon cimma burinmu tare da qwace goruba a hannun kuturu. >Ci gaba a shafi na 2

A Janye Amfani Da Naira 100 Da Gwamnatin Jonathan Ta Buga ­ 4

— MURIC­

Daga hagu: Muqaddashin Babban Kwamandan Askarawan Amurka mai kula da Afirka, Birgediya Janar Leboceuf, Babban Hafsan Hafsoshin Sojin Nijeriya, Janar Gabriel Olonisakin; Babban Hafsan Dakarun Sojin Qasa na Nijeriya, Laftanar Janar Tukur Buratai da kuma Jakadan Amurka a Nijeriya, Stuart Symington yayin rufe babban taron dakarun sojin qasa na Afirka a Abuja, jiya Alhamis.

Fursunoni Masu Xaurin Rai Da Rai Za Bincike: Yin Wanka Kullum Su Yi Digirin Digirgir A Jami’ar NOUN Na Iya Haifar Da Cuta > Shafi na 2

> Shafi na 2

Kotu Ta Halasta Wa EFCC Hana Fayose Amfani Da Asusunsa Na Banki > Shafi na 7


2 RAHOTANNI

A Yau

Juma’a 20 Ga Afrilu, 2018 (3 Ga Sha’aban, 1439)

Fursunoni Masu Xaurin Rai Da Rai Za Su Yi Digirin Digirgir A Jami’ar NOUN Daga Idris Aliyu Daudawa

Wasu fursunoni guda biyu da ke zaman xaurin rai da rai a Nijeriya, Tunwashe Kabiru da Oladipupo Moshood, sun kammala digiri na biyu (da a ke kira Masters), inda a ranar Larabar da ta gabata su ka amshi takardun shaidarsu daga Buxaxxiyar Jami’ar Nijeriya, National Open University of Nijeriya (NOUN). Shugaban jami’ar ta NOUN, Farfesa Abdalla Uba Adamu, ne ya miqa mu su takardun shaidar digirin nasu a gidan yarin Qiriqiri da ke Lagos a ziyarar da ya kai ta gani da ido bisa kasancewar gidan yarin a matsayin wata cibiya ta karatu na tafi-da-gidanka. Haka nan ma wani wanda ke zaman gidan kurkukun na Qiriqiri, Mr Alegbe Afolabi,

ya amshi takardar shaidar digirinsa na farko. Wannan abin tarihi da ya faru ya sanya a hatta shugaban gandurobobi na qasa, Alhaji Jafaru Ahmed, da sauran wasu manyan jami’ai na hukumomin jama’an tsaro da kuma jami’ar sun halarci taron miqa wa fursunoni satifiket nasu. Shi dai Tunwashe ya samu digiri na biyu a kan harkar gudanar da kasuwanci (Business Administration), yayin da shi kuma Moshood ya karanci vangaren zaman lafiya da warware savani (Peace Studies and Conflict Resolution). Don haka tuni Farfesa Abdalla ya yi mu su rijista, domin cigaba da karatunsu na digiri na uku, wato digirin-digirgir (PhD). Su waxanda su ka kammala karatun jami’ar su na daga

cikin xalibai 5,976 na jami’ar da su ka haxa da tsohon shugaban qasa, Olusegun Obasanjo, wanda a watan Janairu ne a ka yaye shi a wani bikin yaye xalibai wanda a ka yi a Abuja. Tunwashe, wanda a ka yanke ma shi hukuncin xaurin rai da rai kuma ya yi shekaru goma a tsare, cewa ya yi, ya na mai imani da ikon Allah watarana zai iya kasancewa a fitar da shi daga gidan Kurkukun. Ya kuma qara bayanin cewar, shi ya na tsammani qwaqwalwarsa ba za ta iya xaukar karatu yanzu ba, amma kuma sai ga maganar jami’ar NOUN, wacce ta bada damar yin karatun jami’a kyauta, ya na mai cewa, idan ba ta wannan hanyar ba da wahala ya yi cimma wannan nasara a rayuwarsa. Tunwashe ya ci gaba da

cewa, “yanzu cikin ikon Allah ni ma Ina da nawa ilimin wanda zan y i alfahari da shi da kuma canza hali na wajen koyon sabuwar rayuwa da kuma mu’amala da al’umma. Ko shakka babu ni ma ban fidda tsammanin Allah zai yi na shi ikon a fitar da ni ba, don na bada gudunwata wajen gina qasata Nijeriya.” Ya yi kira da jami’ar da ta qara samar da wasu abubuwan da a ke buqata wajen taimakawa yin karatun, saboda yin haka zai sa su xalibai su qara maida himmar karatun. Shi ma da ya ke nashi jawabin, Mataimakin Jami’ar Shugaban Jami’ar Mai Cikakken Iko, Farfesa Abdalla ya bayyana cewar ita jami’ar ta na ba wa ’yan fursuna waxanda su ka cxancanci su yi karatun jami’a dama kyauta ne daga

digiri na farko har zuwa digirin digirgir a kuma fannoni daban daban, saboda a samu damar yin karatun jami’a.” Ya qara jaddada bayanin cewa, akwai xalibai 420 waxanda fursunoni ne da ke karatun jami’ar a vangarori daban-daban, waxanda su na karatunsu ne yadda su ka tsara wa kansu ba kuma wasu ayyukan cikin aji waxanda za su damu xalibai. Abdalla ya bada tabbacin cewar jami’ar za ta ci gaba da ganin duk wani fursuna wanda ya cancanci karatun jami’a, sun yi amfani da damar da ita jami’ar ta bada, su qara wa kansu damar da ta samu, saboda idan sun kammala wa’adinsu na zaman gidan kurkuku, za su samu damar yin kyakkyawar rayuwa, domin ilmin da su ke da shi.

• Mahalarta rufe babban taron dakarun sojojin qasa na Afirka a Abuja jiya Alhamis

“Yin Wanka Kullum Na Iya Haifar Da Cuta” Daga Idris Aliyu Daudawa

Masana ilmin kimiyya sun bayyana cewar, yin wanka kullum na iya kusanta yiyuwar mutum ya kamu da wata cuta. Wani qwararre na vangaren cututtukan da su ke saurin yaxuwa daga jami’ar Colombia, Dokta Elaine Larson, ya bayyyana cewar, yin wanka wanda ba a kan qa’ida ba, ya na iya samar wa fatar jiki da ba ta wata dama ta jurewa ruwa ba, na iya sa ta bushe, ko kuma ta zazzage. Hakan kuma zai sa qwayoyin cuta, su samu damar shiga jikin mutum su zama

sanadiyar kamuwa da wata cuta. Larson ya cigaba da jaddada bayanin cewa, mutane su na yin wanka ne, saboda su a gare su hakan zai iya kare su daga kamuwa da wata cuta, amma ya ce abin ba wai ya tsaya ba ne akan hana jiki yin wari ba. Haka nan ma wani mataimakin Farfesa na vangaren nazarin cututtukan da su ka shafi fatar jikin mutum na jami’ar George Washigton, Dokta C. Brandon Mitchell, ya ce, wanke man da ke cikin fata, zai iya samar da matsala na qananan cutukan halitu (bacteria), waxanda qwayoyin

cuta ne da su ke taimakawa garkuwar jiki immune xan adama wajen yaqi da qwayoyin cutar da za su iya cutar da jiki. Mitchell ya bada shawarar cewa yin wanka sau xaya ko biyu ko wanne mako wannan ya isa, amma yin wanka kullum bai kasance dole ba. Ba kuma dole ba ne mutane su sa ma dukkan jikinsu kumfar sabulu ba, amma su maida hankalinsu wuraren da za su iya yin wari, idan ba a yi masu hakan ba, wato kamar hammata. Bugu da qari masu busassar suma su na iya wanke ta, bayan wasu ‘yan makonni, su kuma

masu amosani su na iya wanke kan nasu sau da yawa a cikin mako. Waxannan shawarwarin nasu an haxa su da ilmin da aka samu a wasu bincike – binciken da aka yi, waxanda suka ce yin wanka kullun ba lafiya bace. A wasu bincike binciken da aka yi Dokta Joshua Zeichner, wanda mataimakin Farfesa ne na sashen da ya shafi fatar jikin mutum a asibitin Mount Sinai dake Newyork, ya ce ko sau nawa mutane ke wanka, da kuma bin da suke ganin warin jikin mutum, wannan ya danganci garjajiyance ne.

Shi ma a ta shi gudunmawar wani qwararre kuma masani dangane da cututtukan fata daga Boston, Dokta Ranella Hirsch cewa tayi mutane da yawa suna wanka ne , saboda yadda al’ummarsu suka xauki yin shi wankan. Bugu da qari wani nazarin binciken da aka fitar a watan Janairu shekarar data wuce,sun bada shawarar cewar yawan wanka da yawa yana iya kawo ma bacteria da kuma viruses da kuma ‘bugs masu amfani matsala, waxanda kuma suna zauna ne a jikin mutum bai kuma san da hakan ba.


A Yau

3

Juma’a 20 Ga Afrilu, 2017 (3 Ga Sha’aban, 1439)

ra’ayinmu Matsalar Cin Hanci Da Lalata ‘Yan Mata Kan Cin Jarabawa A Makarantu Sati biyu da suka gabata, kafafen yaxa labarai na yanar gizo sun cika da batutuwa kan wani abin assha na magana da kuma na faifan bidiyo da ya bayyana, inda aka ji aka kuma ga wani Farfesa na Jami’ar, Obafemi Awolowo, (OAU), da ke Ile-Ife, yana bukatar wata xaliba da ta amince ma shi ya yi lalata da ita, domin ya taimaka mata ta cinye jarabawarta. Kamar dai yadda aka zata ne, wannan abin asshan da ya bayyana tabbas zai janyo cece-kuce mai yawa da kuma fusata da nu na qin yarda gami da yin tir daga al’umman Nijeriya. Wasu daga cikin mutanan da suka mayar da martani, sun yi suka ne kan yadda sau da yawa ake cin mutuncin matan ta hanyar neman yin lalata da su. Amma wannan lamarin da ya bayyana na kwanan nan ba shi ne farau ba. A watan Oktoba da ya shige, wani malamin na Jami’a mai karantarwa a Kwalejin Fasaha ta Ogoja, da ke Jihar Kros Riba, wanda yake kuma magidanci ne, hoton sa ya bayyana a faifan bidiyo inda yake neman yin lalata da xalibarsa da yake duba mata takardun ta na kammala karatun ta. Jami’an tsaro ne suka kama shi. Hakanan an ma kama wani malamin na Jami’a, a Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Auchi, tsirara tare da wata xalibarsa. Malamin sai ya yi zargin wai daman cinne ne aka yi ma shi. A wasu lokutan, lalaci da rashin mayar da himma gami da son cin banza na wasu xalibai matan ne ke sabbaba masu hakan. A shekarar 2005, Jami’ar Jihar Legas da ke Ojo, ta kori wani malaminta wanda aka kama daga shi sai xan kamfai, yana qoqarin yin lalata da wata xalibar shi ‘yar aji biyu, a xakin Otel. Batun yin lalata da xalibai mata a makarantu babu shakka abin kunya ne, kuma abin damuwa ne sosai, hakan kuma yakan saka shakku a takardun shaidar gama karatun da Jami’o’i ke bayarwa. Muna tsoron wannan abin kunyan na zargin yin lalata da xaliba mace domin ba ta nasarar cin jarabawa, XBOEB ZB TIBë 'BSGFTB 3JDIBSE Akindele, na sashen qididdiga da ke Jami’ar ta, OAU, da wata xaliba wacce ba a ambaci sunanta ba, wanda tabbas ba shi ne na farko ba, wanda kuma bisa ga dukkanin alamu ba shi zai zama na qarke ba. Domin gane dalilin hakan abu ne mai sauqi. Hakan na faruwa ne kasantuwan su kansu Jami’o’in ba wani abin a zo a gani da suke yi na ganin sun hana aukuwan hakan. Duk da cewa, a dokokin Jami’o’in aikata hakan CBCCBO MBJë OF XBOEB LF EB IVLVODJO

sa na musamman, amma sam ba wasu matakan kirki da suka xauka kan shigen aikata hakan da aka yi a baya, da har zai tsoratar ga sake aikata hakan a gaba. Kasantuwar rashin xaukan wasu matakan hana aikata hakan ne da Jami’o’in ke yi, ga malaman Jami’o’in

da suka aikata ko suka nemi su aikata yin lalata da xalibai matan, ko ma sun aikata xin sun kuma ciyar da su nasarar jarabawowin. Hakan ya janyo rashin dogaro da mahukuntan na Jami’ao’in, inda ta kai wasu xaliban sukan xauki doka a hannun su. Wasu malaman tabbas xaliban sun yi masu

EDITA Abdulrazaq Yahuza Jere

MATAIMAKIN SHUGABA (NA MUSAMMAN) ŚƌŝƐƟĂŶ KĐŚŝĂŵĂ DARAKTAN SASHE DƵďĂƌĂŬ hŵĂƌ

RUKUNIN KAMFANONIN LEADERSHIP SHUGABA Sam Nda-Isaiah BABBAN MANAJAN DARAKTA Abdul Gombe E D E : E Z <d E < ZKZ/ David Chinda D Ez E Z <dK /E < D& E/ Dele Fanimo Felicia Ogbonlaiye DARAKTAN KULA DA MA’AIKATA Solomon Nda-Isaiah Z <d E <h> < ZKZ/E < D& E/ Zipporah D. Tanko D Ez E D E :K:/ Ibrahim Halilu Femi Adekunle Ebriku John

manufarmu

LEADERSHIP A Yau jarida ce da ake bugawa a Abuja. Ta yi tsayuwar daka wajen tabbatar da shugabanci da wakilci nagari. Jaridar za ta ci gaba da kare muradun al’umma, ba kare ra’ayi da muradun mahukuntanta kaxai ba. Da waxannan qudirorin ne muke fatan jama’a za su xora mu kan Mizani. Haka kuma duk ra’ayoyin masu karatu da muke bugawa, ba manufar kamfanin LEADERSHIP ba ne, ra’ayin masu karatun ne. Sai dai, ba za mu tava mantawa da dalilin wanzuwarmu a doron qasa ba, wato: Don Allah Da Kishin Qasa!

cinne ko sun shirya masu shigo-shigo CB [VSë EBHB CBZB TVLB LBNB TV bayan sun yi masu tsirara suka kuma riqa lakaxa masu xan Karen kashi. Duk da shike ana iya cewa, yawanci hakan na faruwa ne bisa yadda zamani ya canza,inda ake ma matan kallon abin da za a yi lalata da su ne kawai aji daxi. Amma kuma a wasu lokutan yanda su kansu matan ke bayyanar da kansu yakan taimaka a nemi yin lalatan da su. Hakan shi ma abin Allah wadai ne. A nan LEADERSHIP JUMA’A, tana yaqi da duk wata manufa ko aiki na cin mutuncin mata ta hanyar yin lalata da su, a ko’ina ne kuwa, kan tituna ne, a kasuwa ne, a makarantu ne ko a wuraren aiki ne. %VL EB ZBXBODJ BO ë KJO CBUVO DJO mutuncin matan ta hanyar neman da malamai maza ne ke yi wa xalibai mata a Jami’o’in, amma da wuya ka ji ana maganan xalibai matan da kan qoqarin jan hankulan malamai mazan domin su yi lalata da su da gangan. Akwai kuma matsalar da xalibai maza kan baiwa malaman cin hanci domin su sami cin jarabawowin na su. Duk waxannan matsaloli ne da ya wajaba a lura da su a kuma nemo hanyar magance aukuwan su. A ra’ayinmu, muna ganin da yawa ko ma duk waxannan matsalolin sun samo asali ne daga irin tarbiyan da mutum ya taso da ita. Wasu lokutan ma sam tarbiyan ce babu. Tarbiya mai kyau takan shirya ta kuma daidaita rayuwar mutane zuwa aikata abu mai kyau ne kaxai. Ya wajaba, iyaye su kula da irin tarbiyan da suke baiwa ‘ya’yayensu wacce ta dace da al’ada da kuma addinin su, su nu na ma ‘ya’yansu maza su daina ganin mata a matsayin ababen xebe sha’awa idan sun girma. Gazawan magance duk waxannan ababen asshan da ke yi mana kisan mummuqe abin takaici ne. hakan yana nu ni da a sake duba tsarin makarantun namu ne, a kuma gyara da kore dukkanin halayen banza daga cibiyoyin ilimin namu. Akwai dai gazawa wajen jagorancin makarantun namu. Malamai da yawa suna karantarwa ne ba tare da an duba cancantar su yadda ya kamata ba. Har sai gwamnati ta xauki matakai kan hakan na musamman, matuqar ana son ganin magance matsalar da sauri. Qwararru sun yi gargaxin cewa, yin musayar bayar da cin hanci ko kuma amincewa da yin lalata domin cin jarabawa,aikin tir ne. Ya kuma wajaba xalibai su qara mayar da hankulansu wajen abin da suke karantawa, domin su gujewa malaman da kan yi amfani da gajiyawan na su, har su nemi yin lalatan da su.


4

A Yau JUMA'A 20.04.2018

Babban Labari A Janye Amfani Da Naira 100 Da Gwamnatin Jonathan Ta Buga, In Ji MURIC •Ko Mene Ne Dalili?

Daga Umar Abubakar Hunkuyi

aikata hakan, sai lamarin ya IBSVĂŞBO "SBCJ OB "KBNJ XBOEB ga Nijeriya. Don haka ya wajaba sanya damuwa ta musamman ke alamta Musulunci, tabbas a janye yin amfani da wannan a tsakanin Musulmi. Mene ne wannan mummunan shugabanci Wata qungiyar Musulmi ta nemi takardar ta Naira 100. dalilin da ya sanya duk lokacin da ne. domin sun bi son ransu na “Ba abu ne mai wahala ba, da a janye yin amfani da takardun Kirista ya zama Shugaban qasa vangaranci ya mamaye daidaiton kuxin Naira 100 da aka buga a mutum ya gane dalilin aikata TBJ BO DJSF IBSVĂŞBO OB "SBCJ da ya kamata su bi. To mene ne wannan abin kunyan. Idandunan zamanin Shugaba Jonathan. “Yaushe mu ukun za mu sake kisan qare dangin in ba wannan Qungiyar kare haqqin Musulmi Jonathan ne suka makance, da TBEVXB OF DJLJO UTBXB XBMRJZB CB %VL DJLBONV NVOB CJZBO ta MURIC, ta bukaci gwamnatin tsagwaron qiyayyar duk wani EB TBVLBO SVXBO TBNB :BVTIF haraji, sannan kuma yawan tarayya da ta janye yin amfani da alami na rubutun larabci, wanda ne waxannan za su kaiwa sauran da muke da shi ya wajabta yin takardan kuxi ta Naira 100 wacce hakan ya sanya bai ma damu da takardun kuxaxen namu da suka la’akari da mu a komai. aka buga a zamanin tsohon rashin nagartan sabuwar da ya saura da alamomin rubutun “A bisa zahirin gaskiya, mu Shugaban qasa Jonathan, kan sanya aka buga ba. Damuwar sa ajami a kansu na, Naira 100, a matsayinmu na Musulmai a abin da ta bayyana da, cire alamar kawai, shi ne ya cika ma wasu Naira 200, Naira 500 da Naiar shirye muke da mu zauna tare da rubutun larabci na ajami da aka tsiraru burinsu na qiyayya da GBSNBLJ OF NVOB TB SBO maqwabtanmu Kiristoci, amma a yi zamanin tsohon Shugaba Musulmi, da suka sha alwashin ganin an cire rubutun ajamin a bisa daidaito, ba da rainin wayo Jonathan xin a shekarar 2014, a kakkave duk wani alami na Farfesa Ishaq Akintola kansu ne da zaran wani Kirista ba. Mun yi amanna da cewa, Musulunci daga farfajiyar kan takardar kuxin. ka ga ashe an yi watsi da milyoyin xin ya sake xarewa kujerar Addinin shugaba, ko waye shi, ba A cikin wata sanarwa da qasarnan. NVMLJO 4IVHBCBODJO RBTBSOBO shi ne abin dubawa ba, matuqar “Ba wannan ne karo na farko ‘yan Arewa ne da aikata hakan. Daraktan qungiyar, Farfesa “An cire rubutun na ajami ne ,P TBJ BO ZJ BO HBNB OF LP TBJ dai zai yi adalci ga kowa. da faruwar hakan ba. Alamomin *TIBR "LJOUPMB ZB ĂŤUBS B UTBLJZBS “A qarshe, MURIC, tana makon nan, qungiyar ta yi tir rubutun ajami da suke kan da babban manufar yunqurin BO HBNB DJONV EB ZBRJO OF EVL da wannan abin da tsohuwar takardun kuxaxenmu tun lokacin kashe gwiwar koyo da kuma dai wannan yana nu na wani abu bukatar gwamnati ta janye gwamnatin ta Jonathan, ta samun ‘yancin kai, a kaikaice aka amfani da harshen larabci, ne shiryayye wanda kuma yake sabuwar takardar kuxin da Jonathan ya buga ta Naira 100, aikata, inda ya ce, cire alamar ta yi ta cire su, a shekarar 2005, wanda shi ne yaren Alqur’ani EB OVĂŤO DJNNB XBUB NBOVGB “A duk duniya, ana yin a kuma mayar da rubutun Arabi ajami ne babban rashin nasarar daga kan takardar kuxi ta Naira mai girma. Wannan magana ce 5, Naira 10, Naira 20 da Naira 50, ta addini. Ba wanda zai aikata takardun kuxi ne da za su dace da na Ajamin da yake kan Naira 200, da gwamnatin na shi ta yi. Ya kuma bayyana rashin zamanin gwamnatin Shugaba haka a Nijeriya sannan ya yi al’adu da kuma tarihin qasa. Sai Naira 500, da kuma Naira 1000. zaton Musulmi za su tafa ma dai kuma, Nijeriya qasa ce mai Muna qara tabbatar da cewa, dacewar sabuwar takardar Naira Obasanjo. “Amma ya kamata ‘yan shi. Amma kamar yadda aka Addinai mabambanta. Don haka, takardar Naira 100 ta Jonathan, 100 da Tsohuwar gwamnatin UB +POBUIBO UB ĂŤUBS EB SBTIJO Nijeriya su san cewa, an yi saba ci mana tuwo qwarya, a yi ashe al’adu da kuma Addinanmu cuwa-cuwa ce kawai. Muna kuma dacewa. Qungiyar ta MURIC, wannan abubuwan ne a tsare da mana rainin wayo da cin kashi, a ne ya kamata a duba, musamman kira da a binciki yadda ta shigo. ta nemi da a mayar da rubutun OVĂŤO IBOUBSBS .VTVMNJ %VL nan ma Shugabanninmu kamar wajen tsara takardun kuxin Muna kuma gargaxi mai gauni alamar ajamin kan takardar cikakken baqauyen Arewa, ba zai kullum sun yi gum sun kasa cewa namu, ko kuma alamomin kan ga duk wani shugaban da zai zo a sarki da makamantan su. nan gaba, da ya nisanci yunqurin kuxin, a kuma janye takardun iya karanta maka komai ba, face VĂŞBO w A shekarar 2005 da Obasanjo “Amma waxancan Kiristocin cire Ajami daga sauran takardun Naira 100 da na 200 da aka buga rubutun arabi na ajami, hakan su a zamanin gwamnatin ta duk wanda yake son yin hulxa ya cire alamomin na ajami a Shugabanni biyun, (Obasanjo da kuxaxen. Ba kuma za mu yi qasa da shi, wajibi ne ya yi da shi ta sabbin takardun kuxinmu na Jonathan), sun kasa fahimtan a gwiwa ba wajen bin dukkanin Jonathan. Takardar jawabin qungiyar rubutun na ajami, hatta rubutun Naira, MURIC, ta yi magana. hakan. Sun dai bar duk wani matakan da tsarin mulki ya yarje na cewa, “Tsohuwar gwamnatin Hausan boko ma ba zai wadatar Amma kasantuwar bayan sa, alami na Turai, wanda ke alamta mana domin dakatar da hakan a Jonathan, ta samar da wata tsakanin ka da shi ba. Don haka Jonathan ma ya zo ya sake ,JSJTUBODJ TBJ TVLB ĂŤUBS EB yanzun ko a nan gaba. sabuwar takardar kuxi ta Naira 100, a ranar 19 ga watan Disamba 2014. Babban abin da ya bambanta ta da wacce aka canza shi ne, cire alamun rubutun ajami daga cikin ta. i :BO /JKFSJZB CB TV HB ĂŤĂŤLPO sabuwar takardar Naira 100 xin ba a kan na bayan ta. Ga ta dai ba ta da nagarta. Sannan kuma tana saurin yagewa. Da ta jima kuma sai ta lalace. Wanda hakan duk ke sanya riqe ta ke da wahala a cikin aljihu ko lalita. “Kan haka, qungiyar ta kare haqqin Musulmi, (MURIC) ta ce, ya zama tilas ta tabbatar da cewa, wannan takardar Naira 110 xin da Jonathan ya buga, sam ba ta dace ba, varnar kuxi ce kawai. Shekaru uku da rabi kacal, da buga sabuwar takardar Naira100 xin, sai ga shi an tabbatar da cewa, ita DF NBĂŤ MBMBDFXBS UBLBSEBS LVYJO da aka tava bugawa a Nijeriya. Wannan babban abin kunya ne Shugaban Qasa Muhammadu Buhari lokacin da yake isa Gidan Friary House, da ke Landan domin halartar taron Qungiyar Qasashe Rainon Ingila.


A Yau Juma’a 20 Ga Afrilu, 2018 (3 Ga Sha’aban, 1439)

Ku kasance tare da tawagar OCTOPUS a TIBöO TBEBSXB na Telegram

TALLA

5


6

TALLA

A Yau Juma’a 20 Ga Afrilu, 2018 (3 Ga Sha’aban, 1439)

Burinmu Shi Ne Mu Sauqaqa Muku

Ba a chaj in kuxin on ka cire d i j a h c a a B saqonnin watin waya k u x i d a g a a k na wasu banku

Da zaran an buxe asusu da mu, za a morewa rashin chaji idan mutum ya cire kuxi a akwatin wasu bankuna, haka kuma ba za a riqa cire kuxin saqonnin waya ba.

Domin cimma nasara a hada-hadar banki, ka yi mu’amala da bankin Sun Trust a Yau Ziyarci: www.suntrustng.com


A Yau

LABARAI 7

Juma’a 20 Ga Afrilu, 2018 (3 Ga Sha’aban,

Kotu Ta Halasta Wa EFCC Hana Fayose Amfani Da Asusunsa Na Banki

Daga Abdulrazaq Yahuza Jere, Abuja

Wata Kotun Xaukaka Qara a birnin Ado-Ekiti da ke Jihar Ekiti ta baiwa Hukumar Yaqi da Karya Tattalin Arziqin Qasa da Zambar Kuxi (EFCC) damar hana Gwamna Ayo

Fayose amfani da asusunsa na banki. Maishari’a J.S. Ikeyegha, wanda ya karanta hukuncin da alqalan kotun su uku suka yanke, ya umurci a hana Gwamnan amfani da asusun ajiyarsa na Bankin Zenith.

Idan ba a manta ba dai, a watan Disambar 2016, Maishari’a Taiwo Taiwo na Babbar Kotun Tarayya da ke Ado-Ekiti ya umurci EFCC ta xage hana Gwamnan amfani da asusun, bisa binciken da ta ce tana yi a kan wasu kuxaxen

da take zargin na qamuyamuya ne da aka zuba a ciki Sai dai da yake EFCC ba ta gamsu da hukuncin ba, sai ta garzaya kotun xaukaka qara domin sake bin kadin lamarin. EFCC ta ce umurnin ya ci karo da wanda

Maishari’a M.B Idris ya bayar a Legas, wanda ya halasta ma ta hana Gwamnan amfani da asusun har sai an kammala bincike. Ko ya za ta kaya a tsakanin Gwamnan da EFCC? Lokaci ne kaxai zai nuna.

Gwamnatin Bauchi Ta Ja Kunnen Masu Zuwa Aiki A Makare Daga Khalid Idris Doya, Bauchi

Shugaban ma’aikatan jihar Bauchi, Alhaji Liman Bello ya gargaxi dukkanin wani ma’aikacin gwamnati da ke sakaci da aikinsa ko kuma masu qin zuwa aiki a kan lokaci ko kuma masu tashi daga wajen aikinsu gabanin lokacin tashi a wajen aiki na zahiri da cewar za su xanxani kuxarsu a hanun gwamnatin. Shugaban ma’aikatan ya yi gargaxin ne a lokacin da ya kai ziyarar bazata zuwa wasu manyan ma’aikatun jihar Bauchi a Larabar nan, domin gane wa idonsa yadda aikin gwamnatin ke tafiya da kuma duba halin da ma’aikata suke ciki domin yin gyara a inda ake da buqata. Liman ya bayyana cewar dukkanin ma’aikacin da bai zuwa bakin aiki ko kuma wanda ke tafi a ba a lokacin tashi ba ko kasu zuwa a makare da cewar suna cin haram, ya nemi ma’aikata da su kasance masu tsarkake albashinsu domin cin halaliyarsu. Alhaji Liman Bello da shi da ‘yan taqagarsa sun isa ma’aikatan muhalli da safiyo ne da misalin qarfe 8.30 na safiya, inda suka samu tarba daga Daraktan kula da sashin mulki na ma’aikatar Alhaji Abdulhamid Mohammed. HOS ya qira yi ma’aikatan da suke aiki a wannan ma’aikatar da su tabbatar da bin dokoki da qa’idojin aiki domin kauce wa fuskantar fushin gwamnati mai ci. Haka kuma tawagar ta Liman Bello ta isa zuwa ofishin shiyya na hukumar ilimi da qarfe 8:55 na safe, hukumar da ke kula da asibitoci na jihar da misalin qarfe 9:20nf, haka kuma ya isa ma’aikatar wuta, fasaha da kuma kimiyya da misalin 9:30nf, inda ya jinjina wa babban sakataren hukumar da ke kula da asibitoci na jihar Bauchi Dakta Abdulazeez Manga a bisa qoqarinsa

na tabbatar da jin daxi da walwalar ma’aikatansa gami da tabbatar da suna gudanar da aiyukansu yadda ya dace domin xaukaka sha’anin lafiya musamman kan qoqarinsa wa manyan asibitocin jihar. Da yake ganawa da manema labaru bayan kammala ziyarar, shugaban ma’aikatan, Alhaji Liman Bello ya buqaci dukkanin ma’aikatan jihar da su sauya halayensu na rashin zuwa aiki kan lokaci ko kuma barin wajajen aikinsu gabanin lokacin da aka xauke su aiki don yi a wajen aiki, ya kuma bayyana cewar bai kamata ma’aikata suke shigo da wasu xabi’u cikin aiki ba, ya

• Liman Bello

buqacesu da su yi amfani da ma’aikatunsu domin xaukan aiki zuwa ga babban mataki don yi wa jama’an jihar hidima. Bello ya kuma fa ce

gwamnatin ba za ta zura ido tana kallon wasu na sakaci da aiyukansu ba, don haka ne ya bayyana cewar dukkanin wani ma’aikacin da bai bin dokoki da kuma qa’idon aikin gwamnati zai fuskacin fushinsu. Ya turanar da ‘yan uwansa ma’aikata kan irin qoqarin da gwamnatin jihar ta ke yi wa ma’aikata musamman wajen biyansu albashinsu a kan qari gami da tabbatar da cewar suna samun yanayin aiki mai nagarta kuma yadda ya dace don haka ne ya nemi su kansu ma’aikatan da su ma a tasu fannin su sanya qoqarinsu don a samu kyautata aiki. Ya kuma sha alwashin

cewar zai ci gaba da sanya dukkanin abun da ya dace wajen dakile xabi’ar nan ta rashin zuwa aiki ko kuma latti a a wajen aiki, ya bayyana cewar dukkanin ma’aikacin da ke sakaci da zuwa wajen aiki ya sani bai cin halaliyarsa, ya nemi kowani ma’aikaci ya ke tsaftace albashinsa ta hanyar yin aiyukan da gwamnati take tsammani daga garesa domin yi wa jama’an jihar hidima tukuru. Daga qarshe ya bayyana cewar gwamnatin jihar mai ci a wannan lokacin za ta ci gaba da tabbatar da cewar kowani ma’aikacinta na samu yanayin aiki yadda ya dace domin kai jihar mataki na gaba kuma cikin nagarta.

Kwamitin Kiyon Lafiya Na Kebbi Ya Ziyarci Fadar Sarkin Kabin Argungu Daga : Umar Faruk, Birnin-kebbi Kwamitin kiwon lafiya a ma’aikatar lafiya ta Jihar Kebbi ya kai ziyarar wayar da kai a fadar mai martaba Sarkin Kabin Argungu, Alhaji Samaila Muhammadu Mera a jiya a Argungu bisa ga shirin nan na asusun kiyon lafiya da gwamnatin Jihar Kebbi ke qoqarin kafawa a jihar. Kwamitin shirin na asusun kiyon lafiya na jihar da ya kai ziyarar a fadar ya haxa da Alhaji Muhammad Nasiru Gwandu a matsayin jagoran tawagar da ta kai ziyarar, wanda sauran mambobbin sun haxa da Mustapha Tata Argungu, Shehu Muhammad daga hukumar WHO, Alhaji Hassan Ibrahim MaiGundi da kuma Muhammad Nasiru Dakingari dukkansu a cikin Kwamitin na wayar da kan jama’a kan muhimmancin shirin asusun kiyon lafiya da gwamnatin jihar ta kebbi ke son vulowa dashi kamar yadda dokar tsarin asusun kiyon lafiya na qasa ya bayar da dama ga kowace jihar a qasar nan na iya yin nata tsarin asusun kiyon lafiya wanda zai iya yin dai dai da jama’arta. Hakazalika, Muhammad Nasiru Dakingari ya bayyana wa masarautar cewa “wannan

tsarin saboda ne shi ya sa aka fara taron masu ruwa da tsaki kan harkar asusun kiyon lafiya a jihar ta kebbi domin tattaunawa kan sabon tsarin da ake son a fito dashi ga jama’ar jihar ta kebbi”. Yace mun kawo ziyara ne a wannan masarauta mai albarka domin ta basu nata shawarwari kan tsarin da akeso a yima wannan sabon shirin domin samar da sauki ga jama’armu a lakacin da duk wata matsala ta asibiti tataso ga mutanenmu. Har ilayau ya nemi masarauta da kuma sarkunan muna gargajiya da su taimaka da kuma bada goyun bayansu ga wannan shirin da gwamnatin Jihar Kebbi ta fito dashi domin amfani jama’armu. Ya ce yanzu ne ake so a tatara bayanai da kuma shawarwari domin mayar da su doka wadda za ta tabbatar da tsayuwar shirin a cikin jihar ta kebbi. Duk masu ruwa da tsaki a harakar kiyon lafiya an sanya su a cikin wannan shirin saboda haka ya yi amfani da wannan dama ta ziyarar faxakarwa kan yadda shirin asusun kiyon lafiya na Jihar Kebbi za ya kasance domin gaya wa sarkin Kabin Argungu, Alhaji Samaila Muhammad mera cewa sarakuna na cikin tsarin wannan shirin domin

• Sarkin Kabin Argungu Alhaji Samaila Muhammad Mera (a tsakiya) yayin ziyarar kwamitin shirin yana tafiya ne daidai tsarin Shari’ar musulumci. Daga qarshe ya kuma amsa tambayoyin da Sarkin Kabin Argungu ya yi domin qara sanin yadda tsarin shirin asusun kiyon lafiya na Jihar Kebbi zaya kasance da kuma wasu tambayoyi da ubannin qasar yankunan masarautar Argungu su kayi. Shi ma da yake jawabain ga Kwamitin asusun kiyon lafiya na Jihar Kebbi da suka kaimasa ziyara a fadarsa da ke Argungu

a jiya yace “ zamu tabbatar da shirin ya samu nasara a jihar ta mu”. Ya kuma bada shawarar cewa a tabbatar da mutanen da zasu jagoranci wannan shirin mutane ne nagari kuma masu mutunci ga jama’arsu. Daga nan ya umurci ubannin qasar yankin masarautarsa da su wayarwa jama’arsu da Kai kan wannan sabon shiri da gwamnatin Jihar Kebbi ta fito dashi domin samar wa jama’armu sauki wurin kiyon lafiya a cikin jihar mu ta kebbi.


8 TALLA

A Yau

Juma’a 20 Ga Afrilu, 2018 (3 Ga Sha’aban, 1439)


A Yau JUMA'A

9

20.04.2018

Madubin Rayuwa BABBAN BANGO

Bikin Baje Kolin FinaFinan Duniya Ya Yi Armashi A Beijing Page 12

AL’ADA

Al’ummar Huli: Qabilar Da Maza Suka Fi Mata Iya Kwalliya Page 10

HANTSI ADON GARI

Dole Mata Mu Qarfafa Juna Kan Sana’a Da Page 16 Karatu – Amina Vatagarawa

Shawarwari Ga Samari Masu Buqatar Aure Page 18

Burina Suna: Umar Faruk Musa Makaranta: Model International. Sunan Mahaifiya: Lubabatu. Burina: In zama Injiniyar gine-gine Aji a makaranta: SS3 Abincin da na fi so: Makaroni da kifi. Shawarata: Mu qaunaci iyayenmu tare da girmama su da yi musu biyayya a koyaushe

Suna: Amal Abdullahi Sunan mama: Zeenaat Abdallah Makaranta: Gora Academy school, Aminu Kano way, Jihar Kano Burina: In zama Likita (Medical doctor) Abincin da na fi so: Fried rice & chicken Kalar da na fi so: Ja da ruwan qwai Shawara ga yara: su girmama na gaba dasu kuma su dage da karatu don su zama manyan gobe.


10

A Yau

Juma’a 20 Ga Afrilu, 2018 (3 Ga Sha’aban, 1439)

ALLAH XAYA GARI BAMBAN

tare da

Aisha Seyoji

08038860634 aysherseyoji@gmail.com

Al’ummar Huli: Qabilar Da Maza Suka Fi Mata Iya Kwalliya A yau mun kutsa cikin duniya in da mu ka yi kicivis da Al’ummar “Huli” Su na zaune a bai ga gariba. Filin namu na yau zai sada ku da mutanen “Huli” wadanda ke rayuwa a yankin “hela” na kasar “papua sabuwar Guinea” kusa da austaralia wanda kuma su ke da haxakar iyaka da ‘indonesia’. Al’ada Al’ummar “Huli” dai sun kasance masu magana da yaren ‘Huli’,tok pisin, sannan da kuma yaren turanci, waxannan mutane sun kasance xaya daga cikin yare mafi girma da yawa a qasar papua ta sabuwar guinea. Mutanen “Huli” sun yi imani da cewa su mutane ne waxanda su ka samo asali tun daga zamanin wani abin bautarsu mai suna “Huli”. ‘Alade’ ya kasance abu ma fi matsayi a wajensu, domin kuwa shine ma ake amfani da shi a madadin kuxi, duk abin da kuxi zai yi. Tofah alade ma zai iya zama madadi kudi. “ Ambua” shi ne sunan da mutanen ‘Huli’ su ke kiran wani “tabonsu” na musamman da shi, wannan “laka” ya kasance abu mai matukar muhimmanci a gare su su na amfani da “ja” da kuma “ ruwan dorowa” wajen banbance jarumansu ta hanyar yi musu ado na musamman da shi a jikinsu. Al’ummar hina su na manya-manyan masaqan huluna ma su gashi irin na al’adarsu da su ke da shi. Akwai asiri da kuma wani abinci na musamman da su ke amfani da shi wajen ciyar da yaro a qoqarinsu na shirya

•Dan Kabilar Huli

•Dakarun Huli

shi zuwa matakin girma ,har ila yau kuma dai domin ganin cewar gashinsa ya yi qarfi da kuma saurin tsirowa. ‘Gashi’ ya kasance abu mai matukar muhimmanci a wajensu. Tirkashi!! Idan aka sami gashin kan yaro sai a riqa amfani da wani sihirtaccen ruwa na su ana fesawa akan wannan gashi har sai ya yi iyakacin tsawon da su ke buqatar ya yi, za’a yayyanke gashin a gyara shi sannan a fidda wani yanayi kamar tsarin hula, iyakacin tsawon lokacin da za’a xauka ana wannan gyara kuwa shine iya adadin lokacin da yaro zai xauka ya na kwana a zaune da taimakon majingini kawai da zai dosa na kansa, domin fannin wannan gyaran kai bai vaci ba. Toh tsugune dai bai qare ba, domin kuwa bayan an xauki kamar tsawon kimanin watanni goma sha takwas ana wannan askin kuma za’a sake rairaye wannan gashi a aske shi sosai sannan a fidda wani ado a jiki kuma kamar qaramar hular gashi, wannan shi ne ya ke nuna cewar yaro ya fito ne daga qabilar ‘Huli’ daga nan kuma za a yi amfani da gashi irin na tsuntsaye waxanda su ka kasance mabanbantan kaloli domin yiwa wannan gashi ko hular kwalliya. Bisa al’ada babu wani abu mai kama da “gado” na sarauta ko mulki, hanyar kaxai da mutum zai kasance mai sarauta ita ce ta hanyar jarumtar shi wannan mutumi a fagen yaqi, yin maslaha tsakanin wasu ma su rikici, da kuma yawan dukiyarka,

•’Yar Kabilar Huli

wannan dukiya dai ba ta kasance komai ba sai tarin “aladu” ko “wuri”. Allah mai girma! Waxannan mutane ba sa tava rabuwa da yaqe-yaqe da kuma tashetashen hankula, a duk kuma lokacin da aka ce wani tashin hankali ya afku har anyiwa wani rauni, toh fa a maimakon ace wannan masifa ta qare, sai kuma a gashi wanda aka yi galaba a kansa xin ya koma domin sake shiri na musamman dan ganin cewa wannan faxa fa lallai bai qare ba, yawanci sukan yi tashin hankali a tsakaninsu ne akan dalilai na su na cikin gida. Yin kwalliya wa jiki ya na daga cikin abubuwa ma fi soyuwa ga wadannan bayin Allah, mata da maza su kan xauki lokaci mai tsawo domin ganin sun wadata jikinsu da Ado. Al’ummar “Huli” sun yi suna sosai kuma sun samu wajen yiwa fuskarsu “fenti”

su kan zana fenti ‘ja’ ko kuma ruwan xorowa a can qasan idanunsu,saman idanu da kuma da kan hanci. Maza su na sanya ‘igiya’ mai kwari wajen tamke qugunsu domin ya riqe musu buxaxxiyar rigar da su ke sanyawa wacce take tsayawa a sama da guiwa, saman ta kuwa akwai dai wata rigar itama a buxe wacce bata kai na qasan tsawo ba, maza su kan suturta tsiraicin su da ganye mai suna “cordyline” wanda ake harhada shi da igiya, su na qara kawata wannan kwalliya ta su ta hanyar sanya ‘yan kunne, sarqar wuya, da kuma wata sarqar da ake yin ta da haqorin “Alade” wanda su ke xaura ta ta bayan wuyansu. Mata su na amfani da fatari mai tsawo wanda aka yi shi da ciyayi wasu lokutan kuwa akan rina waxannan ci ya yi su fito a siffar baqaqe. Laifi ne mai girma a ga mace budurwa ta fito ba tare da ta suturta kirjinta ba,a yayin da kuma bai zama haramun ba ga dattijuwa ta yi yawo kirjinta a buxe, mata su kan yi kwalliya amma ba ta kai yanda maza suke ado ba, akwai kuma abinda ya kasance matan da mazan dukka su na amfani da shi wannan abu kuwa shine wata jaka da su ke amfani da ita, Mata su na amfani da ita wajen xaukar dankali irin na hausawa ,in da a wasu lokutan ma har su kan xauki ‘yayansu a ciki, Maza kuwa ,su na amfani dashi ne wajen xaukar auduga, dankalin hausa a wasu lokutan har da madubi. A kabilar “Huli” maza su na tafiya farauta yayin da mata ke zuwa su nemo hatsi domin

Ci gaba a shafi na

11


A Yau

11

Juma’a 20 Ga Afrilu, 2018 (3 Ga Sha’aban, 1439)

Qabilar Da Maza Suka Fi Mata Iya Kwalliya Ci gaba daga shafi na

10

sarrafa shi ya zamanto abinci Wani abin ban mamaki da waxannan bayin Allah kuwa shine, Mata da maza ba sa tava rayuwa a gida xaya,su na rayuwarsu ne a gidaje dabandaban, akan gina bukkar maza a tsakiyar kauyen yayin da su kuma matayen ,na su bukkokin su na can wajen qauyen. Addini Al’ummar ‘Huli’ sun yi imani da abin bautarsu mai suna “Huli” sun kuma yi imani da cewa yin yanka a zubar da jini shine kaxai maganin duk wata cuta da kuma dukkan wani abin qi, a cewar su cuta da duk wani abin qi ya na faruwa ne sanadiyyar maita,da kuma asiri, saboda haka kuwa idan dai suka yi waxannan yankeyanke to sun tabbata dukkan abinda basa so ba zai afkuba. To amma fah! Bayan bayyanar turawa, kashi sittin da shida daga cikin waxannan mutane su na kirga kansu a matsayin mabiya addinin kirista. Auratayya Kafin ace saurayi ya kai ga zancen aure kuwa sai ya shiga wata makaranta ta musamman da aka yi ta domin koyan yadda ake sarrafa gashi a gyara shi, sannan kuma da yin hula irin tasu ta gashi, to daga nan ne fa saurayi ya ke da damar ya fara farautar irin macen da ya keso ya aura. ‘Yan matansu sun kasance masu muradin auren saurayi fil a leda, toh amma a xaya vangaren kuma, manya mata na cikin gidaje su kan baiwa mazajensu shawarwari su kuma kalailaye su da baki domin ganin cewar sun auro musu yara ‘yan mata ,wadanda su ka kasance masu jini a jika, Hikimar yin haka kuwa itace,a dabara irin ta su shine waxan nan ‘yan mata su ne za su zo su taimaka musu da kiwon “Aladu” da kuma aikin gona. Namiji ya na zama da mace qwaya xaya tal, a lokacin da ya kasance mai qaramin qarfi,yayin da kuwa ya kawo qarfi tofah a lokacin yana da damar qara wasu matan ,mafi yawanci su kan auri mata daga biyu zuwa biyar ko shida, sun yi imani sa cewar arzikin maigida yana qaruwa alokacin da ya auri sabuwar mace,domin kuwa ita wannan sabuwar mace za ta bashi damar qara haihuwa, sa’annan kuma yawan aladu ma da kiwonsu zai qaru, suna aure ta hanyar baiko (wanda suke son juna) ko dai namiji ya gaji mace sakamakon

• Dan Kabilar Huli

mutuwar mijinta, ko kuwa a bashi kyautar matar,lokacin biki akan yi kaxe kaxe da rayeraye,a irin wannan yanayi kuwa har ma wani saurayin zai iya ganin mace wacce ta kwanta masa arai ya nema,zai gabatar da kansa ta hanyar yi mata kyauta. Allah xaya gari banban, ya yin gudanar da wannan biki kuwa za’a shigo da “karuwai” daga garuruwa da suke makwabtaka domin biyawa mazan da ke wajen bukatu, marasa aure har ma da masu auren. Tirkashi ! Ma’ana fa wannan ma yana xaya daga cikin al’adu irin nasu kenan. Dukkanin wadannan hidindumu da ake sha kuwa baya nuna cewa wannan aure ya tabbata domin kuwa mijin zai bada dukiyar aure iyakacin gwargwadon qarfinsa, akan bawa mace “Aladu” goma sha biyar zuwa ashirin da huxu a matsayin kuxin aure, idan kuwa ya kasance cewar aladu su na wahala a wannan lokaci toh “kuxi, wuri ko kuwa “ adda “ wanda aka yi shi da zallar qarfe shine zai zamto a madadin wannan aladu, mijin xa yakasance mai tarin dukiya zai biya kuxin aure mai tarin yawa, wanda kuma ya kasance Dan rabbana ka wadatamu,zai ba da kuxi dai dai matsayinsa,kai harma wanda ba zai iya biya a lokaci xayan ba za’a ba shi aure, amma da sharadin zai biya wannan dukiya sannu cikin hankali. Ango da marya zasu fito da sanyin safiya domin karbar wannan dukiya ta aure,dagana kuma sai magabatan amarya suyi mata

•’Yan Matan Huli

rakiya zuwa sabon gidanta wanda yakasance gidan uwar mijinta ne Bisa al’ada,ango da marya bazasu kasance a gida daya ba,amma kuma ana bukatar ango da amaryar dai su kasance a waje duk sanda sukaji kukan wani tsuntsu,ma’ana koda ace suna cikin gida to fah duk sanda sukaji kukan tsuntsu zau rankayo a guje su fito wannan zai rika faruwa har iya tsawon kwanaki hudu da yini hudu,duk fa wannan al’ amari zai faru ne ba tare da ango ko kuma amaryar sun rintsa ba har na iya tsawon wannan kwanaki,,Wannan aure akwai wahala,to dama ai bahaushe yace sai ansha wuya akansha dadi.. A rana ta biyar amarya da ango za su fito zuwa gona in da amarya zata fito riqe da

abin tono wanda ya kasance kyauta ce ta musamman daga maigidanta,zuwa zasu yi su gyara gonar cikin wani yanayi na tsubbace tsubbace , zasuyi amfani da wannan maroni su tone duk wani kusurwa ta wannan gona,zasu kasance suna maimaita wannan tono har sau biyu wanda a kallah yakan daukesu lokaci kamar tsawon wata takwas. Toh ! Daga nan za’a baiwa ango damar kevewa da matarsa amma kuma hakan fa baya nufin za su ci gaba da rayuwa a qarqashin muhalli xaya,wannan shine ya ke nuna aure ya tabbata ya kuma inganta. Abinci Cimar su ta kasance dankali irin na Hausawa, wanda matan su ke nomawa.


12

Madubin Rayuwa

A Yau Juma’a 20 Ga April, 2018 (3 Ga Sha’aban, 1439)

BABBAN

Bikin Baje Kolin Fina-Finan Duniya Ya Yi Armashi A Birnin Beijing A ran 15 ga wata da dare ne aka bude bikin fina-finai na kasa da kasa na Beijing karo na takwas a birnin Beijing, hedkwatar kasar Sin, inda ya samu halartar shahararrun taurari da darektocin fina-finai da suka hada da Chloe Grace Moretz da ta fito daga Amurka da Chan Ho-San, wato Peter Chan daga yankin Hongkong na kasar Sin da Wu Jing da ya zo daga babban yankin kasar Sin da sauransu. Bikin da ya zuwa yanzu, ya zama wata muhimmiyar alama ta ci gaban fina-finan duniya, da kuma dandalin musayar ra’ayoyi da kuma hadin gwiwa ga masu aikin fina-finai na duniya. A yayin bikin, mataimakin shugaban kwamitin shirya bikin, Du Feijin ya bayyana cewa, tun bayan da aka kaddamar da bikin a shekarar 2010, har kullum bikin na dukufa kan hada karfin masu aikin fina-finai da bunkasa al’adun fina-finai, inda ya ce, “Fina-finai harshe ne na bai daya ga kasashen duniya. Baki kimanin dubu 15 da suka fito daga sassan fina-finai 300 na kasashe da sassan duniya sama da 50 sun halarci bikin, wadanda suka hadu a nan birnin Beijing, don yin shawarwari kan bunkasar fina-finai, matakin da tabbas zai kara ciyar da fina-finan duniya gaba.” A cikin ‘yan shekarun baya, fina-finan kasar Najeriya na samun bunkasa sosai, kasar Sin ta shiga wani lokaci na saurin bunkasa sana’ar. A shekarar 2017 da ta gabata, adadin kudin tikiti na fim mai taken Wolf Warriors II ya samu kaiwa wani matsayin da ba a taba samu a da ba bisa ga kudin tikiti da ya kai RMB yuan biliyan 5 da miliyan 680, wato kimanin Naira biliyan 284 da aka sayar. Baya ga haka, akwai mutane miliyan 159 da suka kalli fim din, abin da ya sanya shi zama zakara ta fannin fim din da ya fi samun masu kallo a kasuwar wata kasa kawai. A farkon wannan shekara ta 2018 kuma, wasu finafinai uku na kasar Sin da suka hada “Operation Red Sea” da “Detective Chinatown II”, duka sun sayar da tikitin da kudinsu ya zarce RMB yuan biliyan 2. Ban da wannan kuma, a wannan shekara, gaba dayan kudin tikitin fim da aka sayar kasar ya kai RMB biliyan 55.9, yawan mutanen da suka tafi sinima don kallon fina-finai kuwa, ya kai biliyan 1.62. Hakan ya sa

•Masu aikin sana’ar fina-finai na Sin da ketare sun taru a gun bikin

kasuwar fina-finan kasar Sin ta jawo hankulan masu sana’ar fina-finai na kasa da kasa da yawa, kana ana ta kara yin hadin gwiwar shirya fina-finai tsakanin Sin da kasashen ketare. Malam Chen Sicheng, wanda shi ne darektan fim din mai taken “Detective Chinatown II”, ya bayyana imaninsa ga kasuwar fina-finai na kasar Sin nan da shekaru 10 masu zuwa, yana mai cewa, “Na gaskata cewa, nan da shekaru 10 masu zuwa, adadin kudin tikitin fina-finai na kasar Sin da za a samu zai kara habaka, sai dai ina fatan karin masu kallo na kasashen ketare za su samu damar kallon fina-finan kasar Sin. Kamar yadda kowa ya sani, yawan kudin tikitin da fina-finan Hollywood suke samu a sassan nahiyar Amurka ta arewa ya kai kaso 30 cikin dari zuwa kaso 40 cikin dari ne kawai na kudin da suke samu gaba daya, wato suna samun ragowar kudin ne daga sauran sassan duniya. Da zuciya daya nake fatan masu aikin finafinai na zamaninmu za su yi kokari tare, don kara samar da fina-finai masu kyau ga duniya.” Mr. Wu Jing, darektan fim din nan Wolf Warriors II a nasa bangare ya ce, masu aikin finafinai na kasar Sin za su ci gaba da

•Chlo&euml Grace Moretz a bikin fina-finai

samar da fina-finai masu kyau ga masu kallo na wannan zamani. Ya ce, “Mun shafe tsawon shekaru uku muna shiryawa tare da daukar wannan fim din, daga karshe mun kaddamar da wannan fim mai kunshe da hotuna 4077, yayin da masu kallonsa suka kai miliyan 159, adadin da ya shaida kokarin da mu masu aikin finafinai ke yi da kuma amincewar da masu kallo na kasar Sin suka nuna wa fina-finan kasar. Don

haka, a madadin dukkanin masu aikin fina-finai, za mu rubanya kokarinmu, don kara samar da fina-finai masu inganci ga masu kallo.” A gun biki kuma, wadannan masu sana’ar fina-finai sun taru a gun dandalin tattaunawar, don tattauna kan manufar hadin kan shirya fina-finai tsakanin kasar Sin da ketare, tare da nazari da tattauna tsari mai amfani na hadin kan sana’ar fina-finai

Ci gaba a shafi na

13


A Yau

Madubin Rayuwa

Juma’a 20 Ga April, 2018 (3 Ga Sha’aban,

13

BANGO

Bikin Baje Kolin Fina-Finan Duniya Ya Yi Armashi A Birnin Beijing Ci gaba daga shafi na

12

tsakanin kasa da kasa. Wasu daga cikinsu sun bayyana cewa, idan ana fatan hada kai wajen daukar fina-finai, to akwai bukatar a kawar da cikas a fannin al’adu tsakanin kasashe daban daban, inda suka bayyana cewa labaru masu kyau shi ne abin da ya fi muhimmanci a fannin. Ya zuwa karshen shekarar 2017, kasar Sin ta riga ta sa hannu kan yarjejeniyoyin hadin gwiwa na daukar fina-finai tare da yankuna da kasashe 20, har ma sana’ar fina-finan kasar Sin da manyan kamfanoni 6 na Hollywood na kasar Amurka sun tabbatar da hanyar hadin kai yadda ya kamata. Stephen Odell, babban daraktan kamfanin SONY Columbia International, na kasar Amurka, wanda ya taba shiga aikin samar da jerin fina-finai na “Spider-Man” da “Men in Black” ya bayyana a yayin dandalin tattaunawar hadin kan fina-finai tsakanin kasar Sin da kasashen ketare da aka shirya a jiya cewa, yanzu suna da shirin daukar wani fim na carton tare da Sin. “Fim na nan gaba da za mu dauka cikin hada gwiwa, zai bayyana labari game da kasar Sin. Za mu nemo wasu labarun na hikayar mafari ko na masu halin musamman na kasar Sin, kamar labari game da Dragon. A ganina, kasar Sin na da babbar kasuwa, gaskiya ta samar da dama masu yawa gare mu domin zuba jari kan wasu finafinan dake bukatar kashe kudi da yawa.” Ko da yake akwai makoma mai kyau wajen hadin kan daukar fina-finai, amma a kullum, ana fuskantar wasu matsaloli a fannin. Daukar fina-finai tare na bukatar a kawar da cikas a fannin al’adu tsakanin kasashe daban daban, kuma kamata ya yi a girmama da kuma bin wasu ka’idojin da suka shafi dokoki, tattalin arziki da kuma al’ummar kasashe daban daban. Kana wajibi ne a daidaita hanyoyin aiki tsakanin masu aikin finafinai. Rob Minkoff, darankan fim na kasar Amurka, wanda ya taba samar da fina-finai na “The Lion King” da “Kings of Kungfu” da dai sauransu, ya bayyana cewa, cimma nasarar wani fim da aka dauka ta hanyar hadin kai na nuna cewa, an yin hadin kai sosai a fannin kirkirar fim din. Ya ce, “A yayin da muke tattaunawa kan fina-finai, gaskiya kamata ya yi mu mai da hankali kan masu kallon fina-finai, ta yadda

• Darektan fim din nan Wolf Warriors II -Wu Jing

za mu rika la’akari da ko labarun da aka bayyana a cikin fina-finai sun samu amincewa a zukatan jama’ar dake bin al’adu iri daban daban. A shekaru 10 da suka gabata, na iso nan kasar Sin don daukar fina-finai, inda na gano cewa, ‘yan kungiyar da nake a kasar Amurka sun hada kai tare da mambobin kungiyoyin kasar Sin sosai. “ Idan an waiwayi kasuwar fina-finan kasar Sin a ’yan shekarun nan, za a iya gano cewa, yawan kudin da aka samu wajen nuna fina-finan da aka dauka ta hanyar hadin kai, abun mamaki ne. Shugaban zartaswar kamfanin Huayi Brothers Wang Zhonglei ya bayyana cewa, saurin ci gaban kasuwar fina-finai na jawo hankulan kamfanonin finafinan kasashen ketare mafi

yawa, don nazari kan yadda za a gudanar da hadin kai da kasar Sin yadda ya kamata. Ya ce, “tun daga farkon shirya fim, ya kamata mu hada kai, misali, mu gayyaci masu sana’ar daga Turai da Amurka don su yi nazari tare da mu, hakan zai sanya fim din da aka dauka tare ya samu karbuwa a kasuwar fina-finan duniya. Na biyu, a ganina, daukar fina-finan carton wata hanya ce mai kyau wajen hadin kan daukar fina-finai, wadda za ta gujewa wasu matsalolin da suka shafi bambancin harsuna, da ra’ayin jama’a da dai sauransu.” Za a rufe bikin na wannan karo a ranar 22 ga wata. A yayin bikin, za a fid da fitattun fina-finan da za a ba su lambobin yabo na Tiantan, za

kuma a nuna fina-finai masu kyau na kasar Sin da ma na sauran kasashen duniya, har wa yau, za a gudanar da taron tattaunawa tsakanin masu aikin fina-finai. A matsayin wani muhimmin bangare na bikin, akwai fina-finai 13 na kasashen duniya da suka shiga takarar karshe ta neman lambar yabon na Tiantan, ciki har da “Barefoot” na kasar Czech da “Dark Wind” na kasar Indiya da “Dog” na Faransa. Baya ga haka, akwai fina-finai biyu na kasar Sin. Ban da wannan kuma, za a kuma sanar da fina-finai 10 da za su samu yabon a yayin rufe bikin da za a shirya a ranar 22 ga wata da dare. (Lubabatu, Bilkisu, Amina Xu, ma’aikatan sashen Hausa na CRI).

• Masu aikin sana’ar fina-finai na Sin da ketare sun taru a gun bikin


14

Madubin Rayuwa

Taskira

Ciwon ‘Ya

Tare da Jummai Ibrahim GSM: 08185137255

Maimaitawa:

Tsaraba Ga Magidanta Kan Biyan Haqqin Aure Daga Edita. A makon da ya gabata mun samu tangarxa wurin rubuta shafin da wannan rubutun ya cigaba, don haka muna baiwa masu karatu haquri sannan muna godiya ga waxanda suka bugo mana waya don neman sake maimaita rubutun, mun amshi buqatarku, don haka ga maimaicin rubutun a halin yanzu: Dangane da yawan tes da wayoyi da muke yawan samu wasu mata ne suke kawo kukan rashin dadewan mazajensu a shimfixa wasu kuma mazan ne ke kukan rashin kuzarin su, to in dai ana so a kiyaye sai an haqura da cin wasu ababen. A saboda haka ne ma dukkan vangarorin da ke da hannu wajen ganin an samu lafiyayyiyar dangantakar zaman aure mai gamsarwa ke qoqari iya qoqari wajen ganin daga vangarensu ba a samu matsala ba. Mijin zai yi qoqarinsa wajen ganin ya tsira da mutunci, girma da darajarsa wajen ganin bai tauye matarsa ba a wannan vangare, haka ita ma matar za ta yi duk mai yiwuwa wajen ganin cewa ta gamsar da maigida a duk lokacin da aka zo tarawa Wannan qoqari da musamman maza ke yi shi ke sanya su a lokuta da dama shaye-shaye abinda suke kira da maganin karfin maza. Wannan kuwa na iya zama na turanci (Viagra) ko na Hausa, irin wadanda za ka ji masu tallan magani a kan tituna da kasuwanni na kwarmata tasiri da ingancinsu Sai dai kuma, waxannan magunguna na qarfin maza na da matuqar illa na kai tsaye ko dai a nan gaba ko kuma a nan take. Misali, maganin qarfin maza na turanci na bayar da kuzari da qarfi ga namiji a lokacin da ya sha, amma illarsa shi ne: zai kasance idan har mutum ya saba da shansa, in har bai sha ba, ba zai iya tsinana komai ba. Na biyu kuma shi ne, zai taqaita rayuwar jima’in mutum. Shi kuwa maganin Hausa dama dai babu wani bincike mai zurfi da aka yi a kai bare a gane adadin da za a sha da zai zama bai yi wa jiki yawa ba. Kuma za ta iya yiwuwa akwai wani adadi na guba a jikin ganye, saiwa ko sassaken

maganin da ya kamata a ce an yi waje da shi kafin a sha mai amfanin, amma sai mu xirkawa cikinmu daga bisani wancan guba ya taru ya haifar da wata lalurar ta daban. Mafita… Sau tari abin da ke sanyawa namiji ya gaza wani katavus na a zo a gani a yayin kwanciyar aure na da nasaba da irin abin da ya ke ci. Maza ya kamata ku fahimci cewa waxanan nau’ika na abinci na da tasiri wajen daqile mazantakarku kuma da zarar kun cire su daga jerin cimarku na yau da kullum, to fa ba sai kun sha wani maganin qarfin maza ba, kuma matayenku za su yi murna da ku, kuma har lau babu wata fargaba ta samun matsalar lafiya sakamakon qoqarin mutunta gida Ga nau’ikan abinci da za ka cire daga jerin abincinka ko kuma ka rage su matukar ragewa 1. Kayan Toye-Toye Nau’ikan abincin da aka toya, kamarsu dankali na Hausa da turawa, kayan fulawa da dai sauran abubuwan da ake toya su da mai wanda suke rage qarfin sha’awar namiji, kai har ma da mace kamar yadda wani bincike na lafiyar jima’i ya tabbatar, A cewar binciken, kayan toye-toyen na nakasta maniyyin namiji ta yadda hakan zai tasirantu wajen hana samun miqewar mazakutarsa yadda ya kamata ko da kuwa an yi masa shafa na sha’awa. 2. Nau’ikan abincin da ke xauke da sinidarin ‘Carbohydrate’. Waxannan nau’ika na abinci sun haxa da gyararren shinkafa da muke kira da shinkafar gwamnati, (shinkafar gida ta fi amfani ga lafiyar jiki da na jima’i). Sauran abincin da ke dakushe kaifin mazakuta sun haxa da ababaden da ake sarrafa su daga fulawa kamarsu burodi, cin-cin, fanke da dai sauransu. Taliyar Indomie da sauran taliyoyi da makaroni duk na iya dakushe kaifin mazakuta musamman idan aka juri cinsu kullum da kullum 3. Nau’ikan Lemukan Gwangwani da na kwalba da na jarka Lemukan na xauke da wani adadi na sikari sama da yadda jiki ke buqata, shi kuma illar sukari na da matukar yawa a jikin Xan Adam. Da farko dai sikari na qara wa mutum qiba, ita kuma qiba na hana namiji kaiwa da komowa a yayin jima’i. Abu na biyu game da sikari dangane da lafiyar al’aurar namiji shi ne, sikari na hana jijiyoyin da ke harba jini zuwa mazakutar namiji a lokacin da yake bukatar haka sai su yi sanyi. Sikari ke jawo matsalar nan da ake kira da illar sikari wato ‘Sugar Crash’ a turance. Idan wannan matsala ta faru, duk tavawar da mace za ta yi wa namiji ba zai miqe ba ko da kuwa yana so a ransa ya yi jima’i. To, mazaje, sai a kula wajen tantance mai za a ci don a tsira da lafiyar jiki da lafiyar aure. Mu haxu a mako mai zuwa cikin yardarm Allah.

A Yau

Juma’a 20 Ga April, 2018 (3 Ga Sha’aban,

Ciwon ‘Ya Mace…

Ciwon ‘Ya Mace…

Sister Iyami Jalo Turaki 08064666847 sisteriyami@gmail.com

Mafita Kan Yawaitar Fyaxe Batun fyade a cikin al’umma ya zama sai addua, iyaye suna cikin tashin hankali dangane da yawaitar faruwar fyaxe dake faruwa a kodayaushe cikin al’umma. Wannan batu abu ne da ke bukatar sa ido da taka tsantsan. A kullum kwanan duniya ana samun sabon labari ga me da faruwar fyaxe, shin ta ina matsalar ta ke ne? Me yake jawo karuwar samun fyade a kullum? Ba wani dalili da za a ce shi ne dalilin faruwar fyaxe a kullum sai rashin tsoron Allah, da kuma bin maganan bokaye, a mafi aksari mutane kan biyewa irin waxannan mutane don neman biyan bukata wanda a qarshe abin baya kyau. Ina Mafita Mafita a nan ita ce : 1: Iyaye su zama masu kula da shiga da fitan yaransu. 2: kar su yadda da yaran makota ko ta unguwa suke fita da yaransu. 3: A duk lokacin da yara zasu fita a tabbatar da sunyi fita ta mutunci. 4: kar iyaye suke barin yara mata da samari kawai su kadaita a cikin gida. 5: kar a bar yara mata tafiya ta barin gari da maza su kaxai komai kusancinsu. 6: Iyaye su kula wurin irin bikin da yaransu mata zasu halarta.

7: Iyaye su daina barin yara mata fita aika da dare. 8: iyaye su yawaita yi wa yara addu’a da neman tsari daga sharrin shaixan. SHAWARA Shawara ga iyaye mata a nan mu sa ni wannan fyade ta zama qalubale a garemu, yana da kyau mu tsaya tsayin daka da addua da kuma sa ido akan rayuwar yaranmu, kasancewar wannan zamani batun fyade ya zama innallilahi wa inna ilahi rajiun! A duniya duka babu wata uwa da zata so ace yau anyi wa ‘yarta fyade, don haka yana da kyau musan da irin mutanen da muke tare da su a makota ko cikin unguwa. Kar mu sake mu qyale su shige shige gidajen makota ko wurin da ba and aike su ba tare da ixni ba. Mu sa ni fyaxe mugun tabo ne da ba ya gogewa a zuciyar wacce aka yiwa har abada, haka duk uwar da ta wayi gari anyi wa yarinyar ta fyade had abada baza ta manta da hakan ba. Mu tsaya sosai don ganin mun samawa yaranmu da mu kanmu farinciki na har abada don ganin mun karesu daga sharrin afkuwar fyade. Farincikin duk wata uwa shi ne samun farincikin yaranta, mu gasgata hakan cikin kowanne yanayi.


Madubin Rayuwa

A Yau Juma’a 20 Ga April, 2018 (3 Ga Sha’aban, 1439)

Raino Da Tarbiyya SADIYA GARBA YAKASAI 08023622757 E-mail: sadiyagarbayks@gmail.com

Sanya Wa Yaro Suna Jamaa Assalamu alaikum. Kamar yadda mu ka saba haxuwa da ku cikin filina mai albarka, Raino da Tarbiyya, yau ma ga mu cikinsa. Dafatan kuna jin daxin wannan filin. Yau zamu faxa kan tarbiyyar yara bayan haihuwa ma’ana da zarar an haife su ana son a ba su suna na gari wanda ya ke a daraja ba irin sunayen da mu ke bawa yaranmu ba, sunan gayu, shi fa yaro duk sunan da ka bashi da shi zai tashi kuma zai iya koyi da sunayen da ba su da asali, ya na da kyau ka bawa yaronka sunan da mu ka tashi mu ka saba irinsu: Abdullahi Usman Umar Aluyu Tasi’u Surajo Muhammadu Mata kuma irinsu Nanakhadija Aisha Rumasa’u Sadiyyah Fatima Jamila Da sauransu, don Allah iyaye a kula da sakawa yara suna barkatai ba tare da an duba ba don Allah. Bayan suna kuma sai uwa da uba su sa ido ga furuci, ya na da kyau a daina furuci marar daxi ga yara don bakin iyaye babbar masifa ce ga yara, sanan a kyautata musu kalami na tarbiyya da biyayya a nusar da su zagi mugun aiki ne. Ya kamata su tashi da salati da tausayi da imani, a ringa yiwa yara shiga ta gari, don Allah kar ayi musu shiga ta banza domin shi itace tun daga xanyen sa ake tankwasa shi don Allah a kula . Shi yaro fa sai da lura domin mu iyaye mata mu ne ma su zama da su fiye da iyaye maza don haka fiye da rabin tarbiyar yara ta na ga iyaye mata yanayin fitar iyaye maza ba mazauna ba ne. Dole iyaye fa su kula yadda wannan rayuwa ta lalace wallahi sai da kula mu duba yara kanana daga shekara bakwai zuwa goma fa yanzu sun iya shaye-shaye wannan abun Allah wadai ne , tilas uwa ta sa ido sosai irin mu’amalar da yara ke yi. Aiken yara da daddare ko da rana shima ya kamata a daina shi don Allah saboda ana lalata yara sosai daga aiken nan, yara mata don Allah asa musu ido tunda yanzu babu imani yanzu a vata maka xanka ko ‘yarka. Ilimin boko da na islamiyyah ya na da kyau yara su fara karatu ana daxa kwakkwafa mu su , don su tashi dai da hali na gari. Allah ba mu ikon bi. Shigar kaya: a ringa sa wa yara kaya na mutunci tun su na qanana don su yi koyi, sannan har girman yara in su na sa kaya na gari to za su tashi cikinsa yarda ki tafiyar da ‘yayanka fa to haka zai tafi . Maza kuma su zamo masu kulawa da iyalinsu, su na bin me suke yi da zarar sun dawo daga kasuwa ko aiki , ya na da daxi uba ya ja xansa a jiki ya na tambayarsa ya ya kaza yaya kaza? Ya zamo da shaquwa da kulawa yarda da zai sa ki ji ki da shaquwa hakan na matukar taimakawa da kula da iyaye , Allah ya ba mu ikon fita haqqin yaranmu. Zamu faxa sashi na gaba wani satin idan Allah ya kaimu, masu bugo waya ga tambayoyi da yabawa ina godiya sosai Allah sa mu dace Mu tara sati na gaba ta ku ‘Yar Mutan Yakasai

Fitattun Mata

15

Tare da Khalid Idris Doya (07069724750) Kidrisdoya200@gmail.com

Fitattun Mata: Hajiya Zulai Abdullahi Daya Ko-Kun-San… Zulai Daya ita ce mai sarautar Sarautar Magaram na qauyen Daya, ta kasance tsohowar malamar makaranta wacce ta yi aiyuka a ma’aikatu dabandaban wacce ta kuma shugabanci makarantun Sakandari, Firamare da kuma makarantun koyar da malamai da daman gaske, ta kuma shugabanci wani kwamiti mai qarfi na bibiyar sha’anin ilimi, wacce ta samu nasara da daman a lokacin da take hidimar aikinta? Wace ce Hajiya Abdullahi Daya?

Zulai

An haifi Hajiya Zulai Abdullahi Daya ne a ranar 1 ga watan Junairun shekara ta 1945 a garin Daya da ke qaramar hukumar Fika a jihar Yobe. Ta fara karatun Firamare xinta ne a garin Daya (Daya Junior Primary School) daga shekara ta 1951 zuwa 1953, sannan kuma ta halarci makarantar ‘yan mata ta Provincial Girls School a garin Maiduguri a tsakanin shekaru ta 1954 zuwa shekara ta 1959, daga nan ne kuma ta hanzarta zuwa kwalejin horar da malamai mata da ke Maiduguri a shekara ta 1961 zuwa 1963, bayan da ta kammala ne kuma sai ta sake nutsa karatunta a wannan makarantar a shekara ta 1965 zuwa 1967, sannan kuma ta sake dawowa kwalejin horar da mata da ke Maidugurin don kara samun wani horo. Zulai Daya ta kuma halarci jami’ar Abdullahi Bayero College a wancan lokacin, wacce a yanzu kuma ake qiran makarantar da suna Bayero University Kano (BUK) daga shekara ta 1967 zuwa 1972, inda ta samu shaidar karatun digiri kan harshen Nasara (Ingilishi). Aiyukanta a ma’aikatu da wurare daban-daban: Zulai Daya ta kasance malamar makaranta a jihar Yobe, inda ta yi aiyuka a wurare daban-daban da suka haxa da koyarwa a Firamaren ‘Damboa Primary School’ daga shekara ta 1962-1964, malamar makaranta a Godowoli Primary School 1965, wata uku kacal ta yi a wannan makarantar, sai ta sake komawa zuwa sakandarin SPS da ke Potiskum a matsayin malama daga 1966 zuwa 1967. Aiyukanta basu tsaya haka ba, ta kuma yi aiki har ta riqe shugabar

makarantar Firamare ta (Kara Primary) da ke Potiskum a 1966 zuwa 1967, ta koyar a sakandarin gwamnati da ke Yerwa a garin Maiduguri a tsakanin shekara ta 1972 zuwa 1973, ta kuma koyar a GGC da ke Maiduguri a shekara ta 1973 zuwa 1978, haka zalika, ta riqe muqamin mataimakiyar shugaban makarantar mata ta GGC da ke Maiduguri, da kuma mataimakiyar shugaban makarantar koyar da malamai ta mata da ke Maiduguri a 1978 zuwa 1979. Shahararta a fannin koyarwa bai kuma tsaya haka nan ba, ta kuma sake zama shugaban sakandarin ‘yan mata GGSS da ke garin Miringa a garin Biyu a shekara ta 1979, shugaban kwalejin koyar da malamai mata WTC da ke garin Nguru a shekara ta 1979 zuwa 1980, haka ta kuma yi aiki a ma’aikatar ilimi ta garin Maiduguri a shekara ta 1980 zuwa 1984, ta sake zama shugaban makaranrar mata ta GGC Maiduguri a shekara ta 1984 zuwa 1985, shugaban makarantar

gwamnatin tarayya na mata da ke Potiskum a shekara ta 1985 zuwa 2001, ta kuma kasance daga cikin haxakar bibiyar sha’anin ilimi tun a 2001 zuwa 2005 a matsayin babbar jami’a. Zulai ta sance a cikin qungiyoyin mata daban-daban da suke qoqarin ilmantar da ‘ya’ya mata da kuma qoqarin xaura su a hanyar da ta dace a kowani lokaci domin su zama mata na gari a rayuwarsu na gaba, haka kuma ta kasance daga mata masu kishin iliminsu, hakan ne ya ba ta damar nutsa dukkanin gudunmawarta a sha’anin koyarwa domin xaukaka darajar ilimi. Hajiya Zulai Abdullahi Daya, ita ce mace ta farko a qauyen Daya da ta fara zurfafa karatunta wacce har ta kawo ga matan da ta taka a rayuwa, wacce hakan ya callata zuwa cikin fitattun mata. Ta yi ritaya a aikin gwamnati ne a matsayin babbar ma’aikaci, inda kuma ta samu sarautar Magaram na Daya. Allah ya Albarkaci rayuwar Zulai da ‘ya’ya biyar da kuma mijinta.


16

17

A Yau Juma’a 13 Ga Afrilu, 2018 (26 Ga Rajab, 1439)

ADON GARI

Tare da Jummai Ibrahim GSM: 08185137255

Dole Mata Mu Qarfafa Juna Kan Sana’a Da Karatu – Amina Vatagarawa A matsayin da al’umma ke ciki a yau, mata sun fi sanin matsalolin kansu da kuma yadda za a warware, shi ya sa masu iya magana kan ce “ciwon ‘ya mace na ‘ya mace ne”. Baquwarmu ta wannan makon ta warware zare da abawa kan buqatar mata su qarfafa junansu kan sana’a, karatu, aiki ko shugabanci: a karanta cikakkiyar hirar: Assalamu alaikum, da farko masu karatu na buqatar ki faxa musu sunanki da tarihin rayuwarki a taqaice… Sunana Amina Lawal Vatagarawa. An haife ni a shekarar 1982. Na girma a Kaduna. Na yi makarantar Nazare a Mary Travis Nursery, na fara Firemare a Makarantar Kaduna Capital School na gama a Essence International School. A can (Essence) na yi Sakandare kafin na tafi karatun Digiri BSc Architecture (fannin zayyane-zayyane) a Jami’ar Ahmadu Bello ta Zariya. Daga nan sai na tafi Jami’ar Cardiff na yi MSc in Environmental Design and then PhD in Architecture (Digiri na biyu a fannin zanen muhalli da kuma Digirin digirgir a fannin zayyane-zayyane) a Jima’ar Newcastle. Yanzu haka kuma ina MSc in Architecture (Digiri na biyu a fannin zayyane-zayyane) a Jami’ar Ahmadu Bello ta Zariya. A shekarar 2011 ina PhD (Digirin digirgir) a UK (Ingila) aka gayyace ni wani BlackBerry group (shafin walwala) tare da wasu mata mu 30. Mun fara kamar social group (shafin sada zumunta) amma sai muka ga kaman za mu iya taimaka wa al’umma idan muka hada kai. To fah daga nan sai mu kai ta sa himma, muka yi CAC registration (rajistar kasuwanci), muka rubuta constitution (tsarin mulki), kuma muka yi ta developing projects (tsara ayyukan cigaba) muna raba aiki. Dayake mu duka Muslim sisters (mata musulmi) ne, sai muka zavi sunan Muslimah Foundation

•Kujerun da Gidauniyar Muslimah ta samar a Makarantar Husna Academy

(wayar da kai) da biyan kuxin asibiti ga marasa lafiyan da suke buqata, sayan equipment da rehabilitation (kayan aiki da gyare-gyaren asibiti) daban-daban. ‘Trash to Treasure’ kuma tarin kayan gida da sawa muke yi daga waxanda ba su buqata mu kaiwa masu buqata, kamar ‘yan IDP (gudun hijira) ko marayu. ‘Sadaqatul Jariah’ kuma muna yi a watan Zul Hijjah ne bisa qa’idojin Sunnah. Ko mu yi borehole (famfo), well (rijiya), gyaran makaranta da sauransu. Second Chance kuma muna zuwa Prison (gidan yari) ne mu tallafa wa masu civil cases (qananan laifi) da basu da gata a Nijeriya kuma aka riqe dan rashin wannan gatan. Na qarshe, kuma mai muhimmanci sosai a qungiyar mu shi ne ‘Ramadan Food Drive’. Yanzu haka mun sa himma wurin shirin shi. Mun kasa project (aikin) kusan kashi 3. Muna ba da daffafen abinci, kayan abinci kuma muna yi wa marayu shirin Sallah. A shekarar 2017 mun dafa abinci a cibiyoyi tara a cikin Nijeriya. Kowane wuri ana raba wa aqalla mutane 100 abinci a kowane. Kowane mutum an qiyasta kashe ma sa Naira 240. Kalar abinci ya danganta da wuri. Misali ‘yan Maiduguri na son kunu, amma a Daura an fi son abinci sosai. Kayan abinci kuma muna dubawa mu ga yawan gida sai a kasa a bada. Wasu mun san su, wasu kuma unguwa muke zava mu yi magana da masu unguwa sai mu raba. Muna sa himma wa mata iyayen marayu. A qarshe kuma muna ma marayu kayan sallah mu xan haxa da kayan abincin walimar Sallah tun da muna da yara kuma duk mun san yanda suke son bikin sallah. Mun ji kin ambaci ‘Blackberry group’, a Ingila ke nan gidauniyar taku take ba a nan gida Nijeriya ba? Muna da membership (‘yan qungiya) kala uku. Akwai ‘silver’, ‘gold’ da ‘platinum’. Silver members suna bin mu a social media: Facebook: Muslimah Globalfoundation, Twitter: @muslimahorg Instagram: @muslimah foundation, Website: www. muslimahfoubdation.com ‘Gold members’ na biyan Naira 1000 a wata bayan bin mu a ‘social media’. ‘Platinum members’ guda 25 ne yanzu. Mu ke shugabancin qungiyar kuma muna ba da aqalla Naira 2000 a wata. Muna da ‘members’ a koi na amma aikin mu shi ne tallafa wa ‘Yan Nijeriya inda muka samu masu mana aiki da hankalinmu ya kwanta

musamman mata da marayu. To ke nan kuna da ofisoshi a sassan Nijeriya kenan tun da kuna da mambobi a garuruwa? A cikin ‘innovative solutions’ (daga cikin hikimomin) da muke gudanar da harkar qungiyar mu shi ne amfani da ICT. Muna da sakatariya a 347 Titin Muhammadu Buhari da ke Abuja amma kusan duka aikin mu a ‘whatsapp group’, ‘Google’, ‘Survey Monkey’ da sauran ‘social media’ muke yi so mun yanke buqatar samun ofis a wuri daban-daban a yanzu. Kuma dayake muna da ‘members’ a koina, kuma muna aiki sosai da wasu qungiyoyi, da ma’aikata muna samun haxin kai da goyon baya wurin implementing (aiwatar da aiki) xinmu. Kowane ‘project’ yana samun tallafi daga Kwamitinmu na aiki, kuma kowane ‘project’ yana da ‘project lead’ a cikinmu wanda take aiki da ko ma wane qungiya ko ‘supervisor’ da muka haxa kai. Shin kuna da wani tsari ne da mace za ta bi idan tana son shiga cikin ku, kuma ya tsarin yake? Kullum muna kiran kowa, mata da maza su shiga ‘Muslimah Foundation’. Ana iya shiga ta website (shafin intanet) xinmu:www.muslimahfoundation. com sai a shiga qungiyar. Ba wahala, kawai za a cika ‘form’. Ta wurin membership (kuxin qa’ida na qungiya) da private donations (gudunmawa) muke samun kuxin yin ‘projects’ dinmu. Alhamdulillah kuma kullun muna koyan aiki kuma muna qara qarfin aiyukanmu. Kuna da naku marayun da kuke tallafawa ne a keve ko kuna yi ga dukkan wani maraya? Ba mu da namu marayun. Shugabannin Muslimah Foundation duka aikin fisabilillah dan neman lada suke yi. Ba ma biyan kanmu kuxi, sai kuxin tafiyar da qungiya kamar ‘website’ xinmu. Ko rent (kuxin haya) ba mu biya. Kowa tana da aikinta da iyali daban da take kula da. Sabo da haka akwai wasu kalan ‘projects’ da suke mana wahala, shi ya sa muke sa himma wurin •Malama Amina Vatagarawa aiki da wasu qungiyoyin ko ma’aikata. Misali muna aiki da ‘Children of Borno’, ‘Husna Academy’, ‘Alyatama wurin ku neman tallafi? Foundation’, ‘Nuruddeen Islamee’, ‘Nurul Iman Islamic Mukan samu haka, amma mun fi bi ta makarantu. Mothers Aid Foundation’, ‘Valley Crest Construction Muna neman wanda suke da qoqari kuma suke neman Ltd’ da sauran su. tallafi. Misali, yanzu idan mace ba ta da miji kuma tana da marayu da yawa a gabanta, za ta iya zuwa

Ko kuna koya wa mata sana’o’in hannu? Muna capacity building (inganta qwazon aiki)

• Amina tare da ‘ya’yanta Ko akwai wani saqo da kike so ki bayar kuma Bamu maki tambaya kansa ba. Muna so mu ja hankalin al’umma da ba da goyon baya wa mata su yi makaranta ko sana’a, tun da idan aka sake su ko mazansu suka mutu, ko suka rasa iyayensu dole su taimaki kansu da yaransu.

amma ya danganta da wane community (al’umma) mu ka je. Misali, wata biyu da suka wuce Business Enterprise (koyon harkar kasuwanci) muka yi tunda duk wani mai sana’a sai ta koya yin kasuanci. Muna yin su sabulu da disinfectant (abubuwan kashe cututtuka) ma. Kuma muna haxawa da jari.

A qarshe wani kira za ki yi ga mata masu zaman jiran a basu? Gaskiya na san mata na qoqari, amma ya kamata mu sa himma wurin tafiyar da rayuwarmu with dignity and integrity (mutunci da kamala). Dole mu tallafa wa mata, mu tashi tsaye mu ba ma juna qarfin guiwa ta wurin neman ilmi, sana’a, aiki ko shugabanci. Mu duka a Muslimah Foundation muna aiki kuma da iyali kuma ga aikin qungiya. Akwai wahala wata rana amma gwamnati ba ta iya komi da kanta, dole kowa ya yi iya qoqarinshi wurin taimaka wa al’umma.

(Gidauniyar Musulma). Waxanne irin aikace-aikace ne Gidauniyar Musulma take yi? A yanzu haka Muslimah Foundation akwai 6 types of projects da mukeyi. 1. Brighter Future (Inganta rayuwa) 2. Health is Wealth (Kiwon lafiya) 3. Trash to Treasure (Fita daga qangi) 4. Sadaqatul Jariah (Sadaka mai gudana) 5. Second Chance (Farfaxo da mutane) 6. Ramadan Food Drive. (Ciyarwa a watan Ramadan) A ‘Brighter Future’ muna tallafawa ma ‘yan makaranta ta wajen scholarship (tallafin karatu), staff salaries (albashin malamai), equipment and furniture (kayan karatu da kujeru da tebura) har da gyre-gyaren makarantu. Muna da xalibai sama da 50 da muka ba ‘scholarship’ a makarantu daban- daban. ‘Health is Wealth’ tallafi ne a wurin kiwon lafiya ta awareness • Haxin gwiwar Gidauniyar Muslimah da Qungiyar Yaran Borno

•Taron Gidauniyar Muslimah a shekarar 2017

•Yayin taron koyar da harkar kasuwanci da Gidauniyar Muslimah ta shirya


18

Madubin Rayuwa

A Yau

Juma’a 20 Ga April, 2018 (3 Ga Sha’aban, 1439)

Hantsi Leqa

Hadari Gabas...

Shawarwari Ga Samari Masu Buqatar Aure Aure babban ni’ima ne a rayuwa. Aure alama ce ta cikar Xan Adam. Aure shi ne silar yaxuwar al’umma. Sannan uwa uba Sunnar Ma’aiki (SAW). Ina samari masu neman aure? Ga shawarwari gare ku: Da farko dai kafin ka fara neman aure, kamata yayi ka sami natsuwa kuma ka nemi yarinyar kirki, ko a cikin ‘yammata nagari ka nisanci guda 3, su ne kamar haka: (1). Tagari ce amma ba ta sonka (2). Uwarta ba ta da tarbiyar muslunci ko kaxan (3) Uwar ita ma ta gari ce amma tana nuna maka matsananciyar adawa Sannan idan ka tashi neman aure ka sani cewa, ko motar da take qarfe wacce za ka riqa hawa ta kai ka duk inda ka keso a lokacin da kake so, dole sai ka samo lafiyayyiya sannan ka koyi yadda ake sarrafa ta, da yadda za ka lallava ta har ta jima maka sosai. Dole ka riqa kula da ita wajen kwalliyarta da gyaran injinta lokaci zuwa lokaci gwargwadon yadda wanda yayi ta ya tsara, kana wanke ta kuma kana ba ta irin man da take sha wanda zai gyara injinta. Kuma in ka tashi yin tafiya ba ka qure maleji ba, bare ta maqale maka a cikin daji ko ta saka ka yi hatsari da sauransu.

To haka mace take, idan ka aura kai ma dole ka miqe da yin wasu hidimomi matuqar kana da buqatar ganin lafiyarta da kwanciyar hankalinka, da zama mai xorewa. Mace za ta riqa yi maka hidima, amma kai ma maigida na qwarai akwai naka irin hidimar. Shin ka auro wacce take sonka ? Idan hark a yi dace ka auri mata tana sonka komai ka ke so za ka samu. Sannan ka zavo mai tarbiyya mai sanin addini da kama kai, mai kunya, bayan haka sai ka fara xora ta a kan hanyar da kai kake buqata, ta tafi a kanta. Amma ka fahimci abu guda xaya. Mace har kullum tana hukunci da zuciyarta ne, tana da tausayi da soyayya da xaukan abu mai hatsari a matsayin qaramin abu. Duk lokacin da zuciyarta ta vaci za ta iya yin komai ba tare da tunanin abin da zai kai ya komo ba. Saboda dogaron da ta yi a kan zuciyarta, shi ya sa komai ilimin mace idan ranta ya vaci ko kuma aka yi mata auren dole za ta iya yin komi. Kenan idan ka auri wace ba ta sonka don Allah ka yi mata uzuri. Ka yi qoqari qaunarka ta shiga zuciyarta sannan ka nemi haqqoqinka. Maigida na qwarai muna yi maka zaton aiki da qwaqwalwa sama da zuciyarka, kana da qarancin nuna

soyayya, da tausayi, ba kamar matarka ba, to amma qwaqwalwarka takan nuna maka me ya dace ka yi? Miji na qwarai ne wanda ya san darajar mace, yake ba ta haqoqinta, idan mace ta yi aiki da zuciyarta to lallai shi kuma sai ya yi aiki da qwaqwalwarsa. Amma ya xauki mace kamar abin hawa kullum sai dai ya yi amfani da ita ba wani kulawa da ita, gaskiya akwai matsala. Yanzu ya za a yi ka zama maigida na qwarai bayan ba ka kulawa da matarka? Ka nemi taimakon Allah (SWT) wajan samun mace ta qwarai, mai

sauqin kai wacce zata tafi dai-dai da buqatarka, sannan ka nemi wacce take son ka, ka zavo mai addini mai son muslunci, ka auro ‘yar namiji ba ‘yar mace ba. Sauran kuma ka baiwa Allah (SWT) ikonsa. Bayan nan ka shirya cewa zaka riqa ganin abubuwan da baka so, amma haka Allah yayi ta dole sai kayi haquri. karka tava saukowa dai-dai da matsayinta, sai gidanka ya lalace. kullum ka riqa cewa ita mace ce kai kuwa namijine to sai a zauna lafiya. Allah (SWT) ya bamu mata nagari, suma matan Allah ya basu maza nagari. Amin.

Lafiya

Sirrin Man Zaitun A Jikin Xan Adam Shi dai zaitun itaciyace mai albarka da kuma bada cikakkiyar lafiya a jikin xan-Adam , kamar yadda muka sani cewa zaitun abune mai daraja, kamar yadda muka samu bayaninta a cikin Alqur’ani mai girma. Haka kuma kamar yadda aka samu daga Hadisan Manzon Allah (S.A.W). An karvo daga sayyadina umar yana cewa, Manzon Allah (S.A.W) ya ce kuyi abinci da man zaitun kuma Ku shafashi a jikinku, domin haqaqa shi yana daga cikin bishiya mai albarka. Daga Cikin Aikin Zaitun Ciwon Ciki Duk mutumin da yake ciwon ciki sai ya samu man zaitun kamar cikin cokali ya haxa da garin habbatussauda ya cakuda ya sha safe da yamma. Yasa mu kamar sati xaya yana sha ko kina sha, in sha Allahu zai bari. CIWON KAI Duk mutumin da yake ciwon Kai to sai ya samu man zaitun yana shafawa a kansa yana kuma shan cokali xaya da safe da rana da dare. Ciwon Haqori Duk mutumin da yake ciwon haqori sai ya samo ganya zaitun da ‘ya’yan habbatussauda ya saka su a cikin garwashi ya buxa bakinsa hayaqin ya

dinga shiga. Ciwon Hanta Duk mutumin da ya kamu da wannan ciwo sai ya dinga shan man zaitun cikin cokali xaya da safe xaya da rana xaya da dare. Ciwon Dasashi Duk mutumin da yake ciwon dasashi sai ya samu man zaitun ya dinga wanke bakinsa da shi. Ciwon Sukari Duk mutumin da ya kamu da ciwon sikari to sai ya samu man zaitun da tsamiya yana haxawa yana sha kafin ya kwanta bacci. Ciwon Asma Duk mutumin da wannan ciwon ya kamashi, to sai ya samu ganyen zaitun ko ‘ya’yansa ya dinga turara wa. Ciwon Koda Duk mutumin da yake ciwon koda, to sai ya dinga shan man zaitun cikin cokali uku a rana. Ciwon Baya Duk mutumin da yake ciwon baya, to sai ya samu man zaitun da garin habbatussauda a kwava ya dinga shafawa a bayan. Ciwon Rama Duk mutumin da yaga yana ramewa, to ya dinga shan man zaitun kullum cokali uku, in sha Allahu zai yi qiba.

Zazzavi Mai Zafi Duk mutumin da ya kamu da zazzavi mai zafi to sai ya dinga shan man zaitun cokali xaya sannan yana karanta Ayatul kursiyyu sau 7 yana tofawa a cikin yana shafe jikinsa dashi. Kyawun Fuska Duk mutumin da yake so fuskar sa tayi kyau, tayi fari wanda bazai cutadda shi ba, to ya dinga shafa man zaitun da man habbatussauda in zai kwanta bacci bayan ya tashi da safe ya wanke da sabulun salo zai yi mamakin yadda fuskarsa zata koma. Zubewar Gashi Duk maccan da gashinta baya futowa sosai ko in ya futo sai ya zuve, to sai ta samu ruwan zafi ta wanne kanta da shi sannan bayan ya xan huce saita zuba man zaitun a hannunta, sai ta shafe kannata da shi gaba xaya kullum. Karancin Jini Duk mutumin da yake da karanci jini a jikinsa to sai ya dinga shan man zaitun cokali biyu a rana. Bayan Gida Mai Kauri Duk mutumin da yake shan wahala in ya zo zai yi bayan gida, wani ma sai yayi kuka saboda wahala, to sai ya samu man zaitun da garin habbatussauda ya kwava sai ya tura shi a cikin duburarsa. Ciwon Mara Ga Mata

Duk matar da take haila tana fama da ciwon mara saboda fitar jini in tana so ta samu saukin wannan ciwon, sai ta samu man zaitun tana haxawa da ruwan tsamiya tana sha, in sha Allahu duk lokacin da zata yi haila bazai mata ciwo ba. Sanyin Qashi Duk mutumin da qashinsa yayi sanyi baya iya motsa shi, to sai ya samu man zaitun da man habbatussauda ya dinga sha yana kuma ya shafawa a wajan. Kyawun Fata Da Laushinta Duk mutumin da yake so fatarsa ta yi laushi da kyau, to sai ya sami man ya dinga shafe jikinsa da shi bayan yayi wanka da ruwan dumi, zai yi mamaki yadda fatarsa zata koma. Qurajen Qarzuwa Duk mutumin da yake da qarzuwa ko wasu quraje, to sai ya samu ganyan zaitun ya kirva shi ya haxa da garin habbatussauda yana shafawa a wajan har ya warke. Ciwon Kunne Duk mutumin da yake ciwon kunne, to sai ya bari in zai kwanta bacci sai a dinga haxa man zaitun dana habbatussauda yana digawa a kunnensa. Ci gaba a shafi na 21


A Yau

Madubin Rayuwa

Juma’a 20 Ga April, 2018 (3 Ga Sha’aban,

Gidan Kowa

19

Tare da Yusuf Shuaibu

Goron Juma’a

08034980391

Assalamu aikum. LEADERSHIP A Yau Juma’a, ina farin cikin da samar mana da dama domin mu sada zumunci ga ‘yan’uwa da abokan arziki. Allah ya qara wa wannan Jaridan tamu farin jini da xaukaka a faxin Duniya baki xaya. Da farko, ina miqa gaisuwar Goron Juma’a ga abokanaina kamar haka Abubakar mai sayar da Kankana a Zuba Fruit Market Abuja, sai kuma Malam Hassan mai Gidan wanka a zuba, tare da Muhammad Abballo mai Computer a Zuba, daga qarshe ina miqa saqon Goron Juma’a ga Abdulrahman Fanteka a Zuba. Da fatan duk suna cikin qoshin lafiya, Allah ya sa haka, amin summa amin. Barka da Juma’a. Daga Abubakar Yusuf, Zariya. 08032337145 Da farko, ina miqa gaisuwar Goron Juma’a ga dangina kamar haka Muhammad Idris, sai kuma Kalifa baba Ahmad, tare da Umar Dogara Inkiya Lauqa-lauqa,da Adon Wanki wato baban Amir da Muhibbat, Oga Ubale Mai wanki da guga, tare da Zubairu Dogi, daga qarshe ina mai miqa gaisuwar Goron Juma’a ga Xan ladi Kalmi. Da fatan duk suna cikin qoshin lafiya, Allah ya sa haka, amin summa amin. Daga Mutala CD Badarawa, Kaduna. 08038685610 Bayan gaisuwa mai tarin albarka, tare da fatan Allah ya xaukaka wannan gidan jarida ta mu, nake miqa gaisuwar Goron Juma’a ga abokan arziki kamar su Salis Kalifa Baba Ahmad, sai kuma babban aminina wato Muhammad wanda aka fi sani da Mamman a cikin garin Kaduna, da kuma Barista Muhammadu Tasi’u Sirajo, da Yunus Abubakar da ke Kaduna, sai Malam Uwaisu Buhari Imam a Abuja, da kuma Muhammad Idris a Lake View Homes Phase 2 a Kado, daga qarshe ina miqa saqon gaisuwar Goron Juma’a ga mai gidan na Raji Musa Yakubu. Da fatan duk suna nan cikin qoshin lafiya, Allah ya sa haka, amin. Barka da Juma’a. Daga Muhammad Kalifa, Kano. 08067325845

Gaisuwar Goron Juma’a ga makusantana kamar su Abubakar Shuaibu, sai kuma Maharazu Shuaibu, tare da Fatima Shuaibu, da kuma Halima Shuaibu, da Yusuf Shuaibu, sai kuma Usman Shuaibu, daga qarshe ina miqa saqan Goron Juma’a ga Kakan mu Hannatu Shuaibu. Da fatan duk suna nan cikin qoshin lafiya, Allah ya sa haka, amin summa amin. Barka da Juma’a. Daga Hajara Usman Shuaibu Badarawa, Kaduna. 08022179656 Bayan dubu gaisuwa mai xabbun yawa ga ma’aikatan wannan gidan Jaridan da kuma

tare da fatan alheri nake miqa gaisuwar Goron Juma’a ga Alhaji Bature mai Lemu Ikara, sai kuma Baba Ibrahim Ikara, tare da Zainab Bature Ikara (Ummu Mus’ab) da Babana Mustapha Lawal, daga qarshe ina miqa gaisuwar Goron Juma’a ga Kwasau Family. Da fatan duk suna cikin qoshin lafiya, Allah ya sa haka, amin. Barka da Juma’a. Daga Ahmad Mustapha, Kwasau. 08036681108 Assalamu alaikum. gaisuwa cikin farin tare da fatan alheri nake ina miqa saqon gaisuwar Goron Juma’a ga ‘yan’uwa da

abokan arziki kamar Sulaiman Yusuf mai kanfanin S.Y Ingawa (LTD), sai kuma Umar Sani Madaki, tare da Musa Yusuf Ingawa wato Acid Quality Designer, da kuma Ibrahim Muhammad inkiya Zola, da Alshak Muhammad, sai Ibrahim Tukura inkiya Shugaban Matasa, tare da Usman Hamisu, sai Adam Ibrahim Xan Barno, da kuma Malam Falalu Abdullahi wanda hake Zaria City, daga qarshe ina miqa saqon Goron Juma’a ga Abba Abdullahi inkiya baka son tsufa. Da fatan duk suna nan cikin qoshin lafiya, Allah ya sa haka, amin sunna amin. Barka da Juma’a. Daga Muhammad Idris, Abuja.

Mahawarar Masu Karatu Ta Wasa Qwaqwulwa Salam, jaridan LEADERSHIP, idan nine ta farko zan bari sai bayan na auri ta biyu sai na dawo in auri ta farkon. Daga Abdulhadi. 09061956867 Salam, LEADERSHIP A Yau Juma’a, to idan nine ta farko zan aura saboda ta yi na mijin qoqari, saboda haka juya mata baya tamkar cin amana ne. Daga Imrana Abubakar mai Jarida, Birnin kebbi. 09034726611

Assalamu alaikum. LEADERSHIP A YAU Juma’a, vangaran filin muhawara. Da fatan Allah (SWT) yayi mana jagora. Mun sani duk mai nunfashi a nan doron duniya ba zai yi ikirari da talauci abin tinqaho ba. Ita wanna yarinyar ta farko wadda ta dalilinta ne na sami damar kamala karatuna da tallafin 1,000 da take karvowa a hannun mahaifinta, sai na saka mata da addu’ar Allah (SWT) ya hore mata wani namiji wanda ya fini. Ni kuma zan karvi wannan tayi na biyu da na samu daga Allah. Daga Ibrahim Ahmad mai Rawani,

Abuja. 08060149092 Salam, LEADERSHIP A Yau barkan mu da Juma’a, ai idan nine gaskiya ta biyu zan aura, sai in bawa waccen ta farko haquri. Daga Alhaji Abdulkareem mai Jarida, Minna. 07033096415 Gaisuwa da jinjina ga dukkan ku da kuka faxi irin na ku ra’ayi. Haqiqa kun yi rawar gani muna godiya.

Sabuwar Muhawara.. Wai idan aka ce daga yau sai yau ka da mata su qara kula maza, kuma ka da maza su qara kula mata, su wa za su fi shiga cikin damuwa, mazan ko matan? Ban da son kai… Mun samu wannan saqo ne daga Mubarak Kaduna, 07032587658 A aiko mana da amsa ta wannan lambar 08034980391 ko ta email xinmu: leadershipayaujumaa@gmail.com sai mun ji daga gare ku.


20

Madubin Rayuwa

A Yau

Juma’a 20 Ga April, 2018 (3 Ga Sha’aban,

Alawar Yara TARE DA UNCLE MUHSIN CIROMA 08104314052 SMARTKID993@GMAIL.COM INTAGRAM: @SMARTKID.SKD_OFFICIAL

YARA MANYAN GOBE

Gwarzuwarmu Ta Xaya

TATSUNIYA Aham! aham!! aham!!! bari in fara da gyaran murya. GA-TA-NAN GA-TA-NANKU Gizo da

Tsohuwa.

Wata rana ne dai gizo yana yawo sai yaga wani katon bijimin sa a daure koda yaga haka sai ya garzaya gidan sarki yaje ya fadi yayi gaisuwa yace shaiki kunnenka nawa, sarki yace biyu, gizo yace kaya (kara) biyu kasha yabayi (labari) yau naga wani katon sha (sa) wanda babu iyinshi a duniya, sarki yace to aje a zo dashi to dama ashe san na wata tsohuwa ce, haka dai sarki yasa aka kwato mata dan san datake ji dashi, da aka yanka san sai aka tambayeta abinda take so acikin naman san sai tace itadai kayan ciki kadai take so da kitse. Da aka bata ta tafi dasu gida ta wanke tukunya ta dora akan wuta tana nufin ya dafu kafin ta dawo daga tallan daddawa a kasuwa. Yar tsohuwa data dawo daga kasuwa sai taga an share mata gidanta fyas, kuma an wanke tsummokaranta har da guga an kuma shiryasu acikin akwati, yar tsohuwa ta rike baki tana mamaki, saboda tasan cewa ita bata bar kowa acikin gidan ba kuma sanda zata fita saida ta kulle gidan tam tam. Daga nan sai ta tafi wajen tukunyar datake dafa nama dan ta gani ko ya nuna ta dan kore mugun yawu, koda ta bude tukunyar sai taga yan mata kyawawa suna mata murmushi, ga wuta tana ta faman ci bal bal amma batayi musu komai ba, sai yar tsohuwa ta rike baki tana mamaki tace to ku fito dama ashe kune kuka share min gida haka? Daga ina kuke? Sai ƴan matan suka ce ai mune naman daki ke dafawa, sai yar tsohuwa tayi godiya ga

Sunanta Hafsat ‘yar makarantar Hil Top Academy Mahaifiyarta Hajiya Aisha Hafsat tana son cin Indomie Malamin da ta fi so Uncle Muhsin

Gwarzanmu Na Biyu Sunanshi Aban G Giwa Sunan Mahaifiya Hajiya Jamila Xan makarantan White Plains British School. Xan garin Sokoto. Aban yana son shan “Pap haxe da Madara” da aka tambayeshi Uncle xin da ya fi so yace “Uncle Ahmad”

Mushaqata

Wani Lambun Shaqatawar Yara a Kaduna

Allah, saboda yanzu ta sami ƴan mata kyawawa wadanda zasu rika yi mata aiki. kurunkus kan xan bere

Kacici-Kacici 1. Me sunan gida da turanci? 2 Mece ce cikakkiyar ma’anar NOUN? 3. Menene Cikakken ma’anar PRIMARY SCIENCE? 4. Yaya sunan COMPUTER da Hausa? 5. Lissafo darasi Bakwai da ake muku a Makaranta... 6. Haqori nawa ne a bakin Xan Adam?

Ka fitar da bambanci guda 7 a jiki waxannan yaran guda Biyu.


A Yau

Madubin Rayuwa

Juma’a 20 Ga April, 2018 (3 Ga Sha’aban,

MATASAN ZAMANI

21

Mukhtar Anwar 0803 667 9084

Kitimirmirar Hana Matasa Riskar Madafun-iko A Nijeriya Da yawan masharhanta na ganin-beken ajin diddigar-qaya na manyan mutane da ke a wannan qasa, na dakushe ko yin qafar-ungulu ga duk wani sanadi da ka iya sahalewa Matasa a wannan qasa riskar manyan kujeru mafiya tsoka na tafiyar da mulkin wannan qasa, musamman kujerar Shugaban Qasa. A na zargin irin waxancan manyan qasa da tsabar nuna kwaxayi da qwalama na karagun mulki, gami da qin son janyewa gefe don sakarwa Matasan mara su mulki qasar, tamkar yadda yake gudana a wannan Zamani cikin wasu manyan Qasashen Duniya, irin su qasar Koriya ta Arewa. Qwalamar son samun xaukaka tutur, tare da begen tara abin-duniya, na daga irin manyan dalilan da ke sanya rukunin Dattijan kin son bai wa Matasan damar da ta cancance su. Alhali ya tabbata cewa irin waxancan manyan qasa sun mori kwatankwacin damar a lokutansu na samartaka. Alhaji Shehu Shagari, ya zama Xan Majalisar Tarayya na qasa yayin da ya ke da Shekarun haihuwa 30 kacal. Sannan, ya yi Minista, yana xan Shekaru 35 a duniya. M.T. Mbu kuwa, ya zama Minista cikin wannan qasa yana da Shekarun haihuwa 25 ne. Sannan, ya zama Jakadan Najeriya a qasar Birtaniya sa’adda ya ke da Shekaru 26 ne kacal. Richard Akinjide kuwa, ya zama Ministan ilmi cikin wannan qasa ne lokacin da Shekarunsa na haihuwa ba su kere 35 ba; Maitama Sule kuwa, yana xan Shekaru 29 ne ya zama Ministan Man Fetur. Bugu da qari, a dai irin waxancan lokuta na baya ne, Audu Ogbeh ya sami damar riqe kujerar Minista yana xan Shekaru 35 kacal a duniya. Saboda yanayi na daven-kwalo,

har zuwa lokacin da ake wannan rubutu (2018), Audu Ogbeh Minista ne a wannan qasa. Matasan Dauri Ne Ja-gaba Hatta A Mulkin Soja Gabanin wannan lokaci da tsoffin kwano ko mutane ke maqalqale da madafun-iko mafiya romo, duk da da’awar da ake cewa masu rinjaye ne ke da iko, tun a wancan lokaci da Soja ke baje-kolinsa son ransa cikin wannan qasa, za a ga cewa Matasan Soji ne ke riqe da akalar qasar. A matsayin tsohon Shugaban Qasa na Soja mafi jimawa a fallen zango guda na mulki, Janar Yakubu Gowon, yana xan Shekarun haihuwa 28 ne ya xare bisa karagar mulkin jagorantar qasar, bayan kifar da gwamnatin marigayi Ironsi. Marigayi Janar Murtala Ramat Muhammad da Gen. Olusegun Obasanjo kuwa, kowannensu ya zama Shugaban Qasa ne qarkashin mulkin Soja, yayinda suke da Shekarun haihuwa 30 da xoriya. Shugaban qasar yanzu (2018) kuwa, Muhammadu Buhari, ta tabbata cewa a wancan lokaci ya zama Shugaban qasa yana da Shekaru 40 da xan motsi ne. Takwararsa ma Janar Babangida, shi ma ya xare karagar mulkin qasar ne alhali Shekarunsa 40 ne da xan motsi. Matasan Yanzu Kuwa Sun Fi Rungumar Harkar Jagaliyanci Kafin mu zo ga bayanin wasu hanyoyin Shari’a da wasu Dattijai cikin qasar ke amfani da, wajen kange Matasan ga barin yin habzi da manyan kujerun mulki a wannan qasa, zai ba da “yar fa’ida yayin qara yin wani xan tsokaci game da harkar Jagaliyanci da ta Ta’addanci da Matasan na wannan Zamani a siyasance suka runguma,

maimakon yin dogon nazarin yadda za a wayigari dolen-dolen a na damawa da su wajen tafiyar da sha’anin mulkin qasar xari bisa xari 100%. Rahoton Kungiyar “International Crisis Group” (ICG), 2007 Qungiyar International Crisis Group, za a ga cewa wata qungiya ce ta qasa da qasa da a har kullum ke nazartar yanayi na tashe-tashen hankula dake kan kwarara cikin da yawan saquna da lunguna na wannan Duniya. Wannan Qungiya ta ICG, ta yi wani dogon nazari game da irin yadda ake amfani da Matasa a wannan qasa wajen afkar da hatsaniya cikin lamuran Siyasar, musamman yayin fuskantowar wani babban Zabe na Du-gari da ake hanqoron

aiwatarwa. A wannan gavar, qungiyar ta ICG, ta yi tsokaci ne game da irin waxancan ayyuka na ta’addanci dake ta kan kwarara a qasar, yayinda Zaben Du-gari na Shekarar 2007 ke qara fuskantowa (Daily Trust, April 2, 2007). Qungiyar ta ICG, ta yi qarin hasken cewa, irin wancan gungu na Matasa da “Yan Siyasar ke amfani da su, za a iske mutane ne da duhun jahilci da qangin talauci yai musu katutu. Waxancan Matasa, za a same su ne da Shekarun haihuwa tsakanin 13 zuwa 19. Sai dai, a kan sami waxanda Shekarun nasu za su kere waxanda aka ambata. (Za mu cigaba, In sha Allah)

Sirrin Man Zaitun A Jikin Xan Adam Cutar Kyasfi Duk mutumin da yake da kyasfi a jikinsa, to sai ya samu ganyen zaitun busasshe, ya daka shi yayi laushi sai ya haxa shi da man zaitun ya cakuxa, ya dinga shafawa a wajen lokacin da zai kwanta bacci. Shafar Aljanu Duk mutumin da yake so ya rabu da aljanu, to ya dinga amfani da man zaitun saboda aljanu basa son shi. Da haka yana da kyau mutum ya lazimci amfani da shi a kowane hali, in da hali ma ya mai da shi mansa na shafawa. Ciwon Karkare Duk mutumin da ciwon karkare yasa meshi, to sai ya samu man zaitun, sannan a samu lalle a kwava, sai a zuba man zaitun din a cikin lalle a gauraya, sannan a karanta (Ayatul Kursiyyu) sau 7 a tofa a ciki sannan sai a tofa a jikin wannan karkare.

Ciwan Nono Duk matar da take fama da ciwan nono, to ana haxa man zaitun da garinsa, a barbaxa akan nonon saboda samun damar zuba, dan qofofin su buxe. Ciwon Saifa Duk mutumin da yake ciwan saifa, sai ya haxa man zaitun da garin habbatussauda da kuma farar saka ya sha. Tsutsar Ciki Duk mutumin da yake da tsutsar ciki, to sai a samu man zaitun da garin habbatussauda da zuma ya kwava su ya sha, wannan tsutsar zata mutu. Ciwan Hanji (Ulcer) Duk mutumin da yake da gyanbon ciki, to sai ya samu garin habbatussauda kamar cokali xaya sannan ya samu garin (kumasari)da ganyan zaitun mai laushi ya jiqa su ya

dinga sha har sai ya warke. Fitsarin Kwance Duk yaro da yake fitsarin kwance, to sai a samu garin zaitun da na habbatussauda a zuba a nono a dinga bashi yana sha zai daina. Mutuwar Jiki (Kasala) Duk mutumin da jikinsa yake yawan mutuwa to sai ya dauwama yana shan zuma da garin habbatussauda zai ji qarfin jikinsa. Yawan Zazzavi Duk mutumin da yake yawan yin zazzavi, to sai ya samu garin habbatussauda kamar cikin ludayi ya kwava da ruwan zafi, da kuma zuma mara haxi ya dinga sha. Cuwon Gavovi Duk mutumin da gavovinsa suke ciwo to sai ya samu garin habbatussauda da zuma ya dinga sha, sannan kuma ya zuba garin

habbatussauda a cikin man zaitun ya dinga shafawa a gavovi. Qwarqwata Duk matar da take fama da qwarqwata kuma har take son rabuwa da ita, to ta samu man zaitun da garin habbatussauda ta kwava sannan sai ta bari sai rana ta take sai ta zubar wannan man a kannata ta bar shi yayi kamar minti (20) sannan sai ta wanke. TARI Duk mutumin da ya kamu da kowanne irin tari, to sai ya samu garin habbatussauda da man zaitun da ‘yar citta da tsamiya da zuma, sai ya haxa su guri xaya ya cakuxa ya dinga ci. Majinar Qirji Duk mutumin da yake yawan majinar qirji to sai ya samu man zaitun da garin habbatussauda ya haxa ya dinga ci kullum sau biyu (2) safe da yamma.


22

Madubin Rayuwa

A Yau Juma’a 20 Ga April, 2018 (3 Ga Sha’aban, 1439)

Tare da UMAR MUHSIN CIROMA umarmuhsin993@gmail.com 08104314052 Instagram: Smartkid.skd_official

Rai Dangin Goro

MAI IDO A TSAKAR KA

• Jirgin Xanfulani

•A-kasa-a-tsare

•Babban kwastama

•Uwar kasada

•Kurar zamani

•Ba a wasa da ciki

•Abin duniya ya ishe ni

Mu Qyaqyata Wani mutum ne yana cikin otal, sai ya duba xakin da ya sauka, sai ya ga akwai kwamfuta. Saboda haka sai ya hau online domin ya tura ma matar sa sako ta E mail. To ashe ya yi kuskuren shigar da saqon a wani adireshi wanda ba na matarsa ba, na wata matar ce daban wadda mijinta ya mutu, a dai-dai lokacin domin a lokacin ma ba a fi awa xaya da kai shi makwancinshi ba. To sai matar nan ta hau kwamfuta domin ganin saqonnin ta’aziyyar da aka turo mata. Tana gama karanta saqo na farko •Aurenmu zai yiwu kuwa?

sai masu amsar gaisuwa da ke tare da ita suka ga ta faxi a some , suna duba kwamfuta suka ga saqo kamar haka “Zuwa ga matata na san za ki yi mamakin ganin wanan saqo nawa to ba abin mamaki ba ne, domin gaskiya wurin yana da kyau saboda akwai duk wani abun more rayuwa, har da kayan alatu, saboda haka ke ma na gama shirya miki komai, gobe za ki biyo ni domin mu ci gaba da zama tare...... Su ma masu ta’aziyya suna gama karantawa sai gudu!! Gaskiya mata babu amana da namiji ne har bankwana zai yi da kowa kafin goben saboda zai je gurin matarshi. Mata kun yarda namiji ya fi ji da matarsa?


A Yau Juma’a 24 TALLA

20 Ga Afrilu, 2018 (3 Ga Sha’aban, 1439)

TALLA 23

A Yau Alhamis 19 Ga Afrilu, 2018 (2 Ga Sha’aban, 1439)


24

Madubin Rayuwa

Magunguna A Musulunci facebook: Magunguna A Musulunci

A Yau

Juma’a 20 Ga April, 2018 (3 Ga Sha’aban, Dakta Jamil Nasir Bebeji 07017790084 magungunaamusulunci@gmail.com

Bayanin Ciwon Sanyi Mai Suna ‘Chandroid’ To shi ma wannan ciwon sanyin yana da haxari, don yana daga cikin cutukan sanyi da yake damun mutum, da jin zafi yayin yin fitsari, kuma mafi yawancin wanda suke kamuwa da shi, ba sa daxewa suke kamuwa da ciwon ‘Sifils’. Shi ma cikinta wani yake bayani a Mujallar ‘Digest’ 1987 cewa a mafi yawa kashi 50 na waxanda suka kamu wannan ciwon sanyin, suna xauke da ‘Sifilis’. Haka dai acikin ita wannan Mujallar ta Digest da take fita a qasar Ingila, da ta a watan Afrilu 1989. Dr. Wilcos yake cewa, a wannan shekarar alqaluma sun nuna a duniya gaba xaya shi wannan ciwon sanyi ya fi ko wane ciwon sanyi yaxuwa a cikin mutane, wanda sai ka ga a cikin kashi 100 na masu xauke da cutukan sanyi kashi 26 duk masu irin wannan ciwon ne. kuma aka qara wani binciken a London a shekara ta 1999, inda aka gane cewa mafi yawancin masu xauke da shi matasa ne, ina ganin ko dalilin haka shi ne, saboda matasa su suka fi jin motsawar maniyyi mai qarfi, kuma gasu ba su da isasshiyar dabarar da za su iya gane mai ciwon ballantana su kare kansu daga jima’i da mai ciwon. Kuma yana daga cikin babbar illar wannan ciwon bai bar yara ko jarirai ba, ballantan tsofaffi. Wato dai a taqaice yana kama ko wane

irin mutum, mace ne shi ko namiji, matashi ko tsoho ba banbanci, sai dai ya fi kama matasa. Sannan shi wannan ciwon sanyi ‘Kalamidial’ yana illar cewa sai ka ga sanda aka fara shan magani musamman in maganin mai kyau ne da yake iya yaqar ciwon ya kashe shi, sai a ji a farkon lamari ciwon yana qara zafi kamar ba zai tafi. Shi ya sa wasu za ka ga suna ta yawon neman magani daga nan zuwa can, saboda sun fara shan maganin sun ji ciwon yana qaruwa, sai su barshi su tafi wurin wani mai maganin. Shi wannan ciwon tsohon ciwo ne, tun da alamunsa yake bayyana a tare da mutum idan ya kamu da ciwon. An gamsu a rubutun magabata likitocin da suka rayu tun wanda ya zo Bukhari da Muslim, “Masalul muminina fi tawaddihim, wata’axxufihim watarahumihim, Masaluljasadi jasadi izashtaka minhum adhuwun tada’a sairuljasadi bissahari walhumma”. Wato misalin musulmai masu imani wajen soyayyar junansu, da kyautatawa da kula da junansu, da tausayin junansu na cewar duk abinda ya samu xau uwansu kamar su ya samu, kamar misalin jikin mutum ne idan wata gava ta yi ciwo, ko ciwo ya kamata, sai ka ga duk sauran jiki ya kamu da damuwa, da rashin bacci da zazzavi, wannan fa bayanin likitoci ke nan. Saboda

haka, shi ma sakamakon wannan ciwo da ya kama wani vangare na jiki ne ko dukkansu wannan zazzavi yake bayyana. To bayan bayan zazzavi ne sai wani xan qullutu ya bayyana a jiki musamman hammata, ko mats-matsi, ko a zakari ko ‘ya’yan maraina, ko farji, amma ya fi bayyana a zakari ko farji, sai dai a farko lamari bay a zafi, don wani lokaci ma sai ya bayyana ba a ma san ya bayyana ba har ya baje ya tafi, ko da ba a yi magani ba, tunda sharri yake shirya wa mutum. Bayan ya tafi da ‘yan wasu kwanaki sai ka gaya dawo da gaske, don wancan zuwan shin a baya kawai ni’imar Allah Ta’alah ce ga bayinsa, sadan ya bayyanar da shi don in akwai ilmin da ya sa aka gane abin, to a yi sauri a nemi magani tun bai yi qarfi ba. To daga lokacin da yayi bayyana ta biyu ne za a fara zub da farin ruwa kamar madara ta gaba, sakamakon qurarraji da suka haifu a can cikin mafitsara, sannan kuma za a fara jin zafin fitar fitsari sosai a mafi yawa, inda za ka ga in mutum ya zo yin fitsari yana jin zafi mai ciwo da zogi. Kuma ko da bayan ya gama sai ya ci gaba da yi masa raxaxi, sannan fitsarin ka ga yana fita kaxankaxan ana yinsa a kai-a-kai, ka ga mutum yanzu zai je yayi fitsarin to kumayana dawowa ba zai daxe ba

sai ya qara jin wani. Amma shi ma jin zafin a mafi yawa ‘yan kwanaki kawai yake yi ya tafi, ko ba a nemi magani ba, amma ba wai ya warke bane. Shi ne Dr. Muhd Ali Bar a littafinsa ‘Al’amradhul jinsiyyah, assababuha wa ilajiha’, yake cewa, ba ciwon da sanyi mafi sharri kamar shi wannan ‘Kalamiyal’. Saboda zafin da zoginsa, sai ka ga yana hana mutum nutsuwa a duk al’amuransa, hatta ko cikin Sallah da ake son nutsuwa wani yana sallah fitsari yana xugowa, kuma ga zafi. To daga nan ne sai kumburi ya dunqulalle ya bayyana ya turo mara kyan gani, ko dai a harshe, ko a hammata, ko a gaba, ko a matsematsi, kuma ya kan bayyanar da quraje wani lokacin a wani gefe na jiki musamman ga maia xabi’ar Saudawi wato daga nan ne mutum duk wata sha’awarsa sai ta tafi ko ta ragu, sha’awar jima’i da ta abin sha, da bayyana rauni a gaba xayan jikinsa, da bayyanar ciwon baya da gavovi. Kana in ba a warke da wuri bashi shi ma za ka ga qafar mutum tana qatuwa kamar ta giwa. Bayan Allah masu karamci, rigakafin guda biyu ne, addu’a da kuma cewa kada mutum ya sake ya sadu da wadda ba a riga an gwada su ba, ga masu sabon aure ke nan. Amma ga ma’aurata sai a gujewa zuwa wajen cuwa-cuwa, saboda ta hanya xaya kowa yake iya xaukarsa ita ce jima’i, savanin sauran ciwon sanyi da za a iya xauka ta hanyar fitsari a wurin da mai ciwon yayi fitsarin, kuma shi ana iya xaukarsa ta baki ma yayin da aka sumbaci juna, wato ‘Kiss’ haka kuma ta hanyar yin Luwaxi, ko Maxugo, magninsu shi ne:- Yusjam, Aulama, da Sihhatuzzaujaini, wato lafiyar ma’aurata, da duhumul jald, da Harqu, suna da cikakkiyar tasiri akan wannan ciwon da wasunsu da za a warke gaba xaya da iznin Allah Ta’alah. Kuma mun tanaje su gaba xaya sai dai kawai a zo a karva a cibiyar mu ta Alyusra dake Kano Unguwar Na’ibawa, da Dutsen Jihae Jigawa Hakimi street, da Jihar Nasarawa Abacha Road, da kuma Abuja Garki Village daura da masallacin ‘yan Izala.


A Yau

Dausayin Musulunci 25

Juma’a 20 Ga April, 2018 (3 Ga Sha’aban,

Sayyid Isma’il Umar (Mai Diwani) 08051529900 (Tes kawai)

Girman Darajar Manzon Allah SAW (5) A uzu billahi minas shaixanir rajim. Bismillahir rahmanir rahim. Wa sallallahu alan Nabiyyil karim. Assalamu alaikum warahmtullahi Ta’ala wa barkatuh. Masu karatu barkan mu da sake haxuwa a wannan makon. Idan ba a manta ba a karatunmu na makwanni biyu da suka gabata mun yi bayani a kan Gwarzon Musulunci a qarne na 20, wato Shehu Ibrahim (RA) saboda zagayowar watan da aka haife shi. A wannan makon kuma za mu xora karatunmu na baya, wato Girman Darajar Manzon Allah (SAW) kashi na biyar. Allah Tabaraka wata’ala ya cigaba da cewa “Haqiqa (Manzon Allah) ya gan shi (Mala’ika Jibrilu) a sasannin mahudar rana mabayyani”. Sai dai lamirin da aka yi amfani da shi a cikin ayar, wataqila an ce fassararsa “ya ga Ubangijinsa” ne. Sayyidina Abdullahi bin Abbas da wasu daga cikin Sahabbai (RA) suka ce Manzon Allah ya ga Ubangijinsa ne. Waxanda suka kafa hujja da maganar Sayyada Aisha (RA) kuma suka ce “ya ga Jibrilu” ne. Sayyada da ta ce Manzon Allah Jibrilu ya gani, amma ba cewa ta yi Manzon Allah ne ya faxa ma ta ba. Ijtihadi ta yi ta fassarar ayar “Ido bai riskar ganin Allah…”, idan Sahabi ya kawo abu, sai aka samu maganar Annabi (SAW) a kai, toh shikenan sai a karvi na Annabin. Akwai Hadisin da Manzon Allah (SAW) ya ce “na ga Ubangijina”, kun ga yanzu wannan ya warkar. Idan bai inganta ba (Hadisin), to maganar Abdullahi bin Abbas a kan Manzon Allah ya ga Ubangijinsa ta inganta. Idan aka samu Sahabbai biyu, wannan ya ce akwai; wannan ya ce babu, to sai a xora na wanda ya ce akwai a kan na wanda ya ce babu. Abdullahi bin Abbas ya tabbatar da cewa Manzon Allah (SAW) ya ga Ubangijinsa. Ya ce ai abubuwa ne guda uku. Annabi Ibrahim (AS) an bashi Badaxantaka, Annabi Musa (AS) an bashi

–jin- maganar Allah, shi kuwa Annabi Muhammadu (SAW) sai aka haxa ma sa jin maganar da gani. Hadisai ne da yawa a wurin. Kuma Malamai suka ce da yawa masu kafa hujja da cewa Manzon Allah bai ga Allah ba, suna kawo ayar “Ido ba ta riskarsa (SWT)”, gaskiya ne wannan, domin hakan ita ce Aqidarmu ta Musulmi. Amma Malamai sun ce ma’anar ido ba ta iya riskarsa (SWT) ana nufin ido ya kewaya shi, wato mutum ya gane Allah ciki da bai. Sai dai babu laifi Allah ya nuna wa Manzon Allah (SAW) abin da ya dace da muqaminsa. A kwanan baya mun kawo maganar Shehu Ibrahim da ya ce in dai Malamai sun yarda cewa Manzon Allah ya ga Jibrilu mai fukafuki dubu xari shida, kuma ko wane fukafuki ya rufe duniya, ai an san ba irin sauran idanun da aka sani ba ne kamar na ko wane Xan Adam. Don haka babu mamaki a ce Allah ya nuna wa Manzon Allah (SAW) Zatinsa. Ko kuma Malamai suka ce ma’anar ido ba ta riskar Allah kamar misali ne mutum ‘ordinary’ ba zai iya zuwa kai tsaye ya ga shugaban qasa ba, amma idan shugaban qasa ya ga dama ya ce a zo da wannan mutumin fa? Akwai mai hanawa? To haka nan Xan Adam zai iya ganin Allah idan Allah da kansa ya riskar da shi, ma’ana yadda ya yi wa Manzon Allah (SAW). Don haka ayar ba ta hana ganin Allah da Manzon Allah ya yi ba. Al’ummarmu (Musulmi) an tafi a kan cewa a nan duniya zahiri ba wanda zai ce ya ga Allah, sai dai a lahira. Manzon Allah (SAW) ya ce “Za ku ga Allah (a lahira) kamar yadda kuke ganin wata a sama babu mai ture wani (balle a ce wani ya kare wa wani)”. Amma kuma a nan duniya za a iya ganin sa a mafarki, domin mafarki xan sababi ne. Imamu Shafi’i (RA) ya ce “sai da na ga Allah sau xari a mafarki”. Sahabin Manzon Allah Abu Juhaifa (RA) ya zo ya gaida Manzon Allah da safe, sai

Shehu Ibrahim (RA) ya ci nasara wajen yin kira zuwa shiga addinin Musulunci da hikima da wa’azi mai kyau da jayayya mafi kyau

Manzon Allah ya ce ma sa “Abu Jhaifa ya ka kwana?”, sai ya ce “Ya Rasulallahi na kwana mai yaqini, na sakankance da duk abin da ka faxa na yarda da shi”. Sai Manzon Allah (SAW) ya ce “Abu Juhaifa, idan mutum ya faxi abu fa sai an tuntuva an ji, meye ma’anar yaqini?”. Abu Juhaifa ya ce “Ya Rasulallahi kamar na ga qiyama ta tashi, ga Al’arshin Allah (Tabaraka wata’ala), ga Allah yana hisabi. Na ga xan wuta a cikin wuta, na ga xan aljanna a ciki.” Manzon Allah (SAW) ya ce “ka sani, riqe (abin da ka sani)”. Don haka, Malamai sun kasu kashi biyu a kan wanda Manzon Allah (SAW) ya gani. Wasu suka ce Jibrilu ne da surarsa, wasu kuma suka tafi a kan cewa Manzon Allah ya ga Allah ne (Tabaraka wata’ala) ba Jibrilu ba. Aya ta gaba “wa ma huwa alal gaibi… (zuwa qarshe)” ta ce, “Manzon Allah (SAW) bai zamanto a bisa gaibin Allah abin tuhuma ba”. Abubuwan da aka aiko shi da shi na Manzanci ya isar. Idan kuma aka tafi a kan wata qira’ar (wadda ake

amfani da zhwa’un ko a ce xamisahannu mai xigo), ayar tana nufin Manzon Allah ba abin tuhuma ba ne. Wata fassarar kuma tana cewa ayar tana nufin Manzon Allah ba mai rowa ba ne a bisa abin da Allah ya kimso ma sa (gaibi). Abin nan da Allah ya kimsa ma sa bai yi wa sauran halitta rowa ba, ya yi kira zuwa ga Allah. Yadda aka kimsa ma sa haka ya sanar da al’umma (SAW). Duk wannan yabo ne da Allah (SWT) yake yi wa Manzon Allah (SAW). Kuma hakan yana nuna mana girman darajarsa (SAW). Allah ya tunatar da mu da irin hikimomin da ya kimsa a cikin Manzon Allah (SAW) da iliminsa. Wannan ayar ta “wama huwa…. (zuwa qarshe)” duk Malamai sun yi ittifaqin cewa tana magana ne a kan Manzon Allah (SAW) babu savani. Babu wani da ya ruwaito Hadisi cewa ayar tana magana ne a kan Mala’ika Jibrilu (AS). Za mu dakata a nan sai Allah ya kai mu mako mai zuwa. Wa sallallahu alal fatihil khatimil hadiy wa ala alihi haqqa qadirihi wa miqdarihil aziym.


26 LABARAI

A Yau Juma’a 20 Ga Afrilu, 2018 (26 Ga Sha’aban, 1439)

An Tsinci Sandar Majalisar Dattawa A Hanyar Maraba Daga Khalid Idris Doya, Abuja

Rundunar ‘yan sandan Nijeriya ta samu nasarar kuvuto da sandar iko ta Majalisar Dattavan Nijeriya wacce wasu da ba a san ko suwaye ba suka kutsa majalisar gami da sacewa a sa’ilin da majalisar take tsaka da gudanar da zamanta a ranar Laraba, waxanda ake zargin da sace sandar ikon sun kai mutane biyar. Muqaddashin babban jami’in hulxa da jama’a na rundunar ‘yan sandan Nijeiya Sifiritanda Aremu Adeniran shi ne ya shaida hakan a cikin sanarwar manema labaru da ya aiko mana da sanyin safiyar jiya Alhamis, ya ce sun samu nasarar kovutar da sandar ikon ce a qarqashin wata gada da ke mashigar Abuja. SP Aremu ya bayyana cewar, aukuwar satar sandar ikon ke da wuya ne kuma shugaban rundunar ‘yan sandan qasar nan, (IGP) Ibrahim Idris ya bayar da dukkanin umurni gami da qarfin iko ga sashin qwararru na rundunar da ke qarqashin sashin bibiya na IGP, domin su samu nasarar qwato sandar cikin gaggaawa. Aremu Adeniran ya kuma shaida wa manema labarai cewa, shi shugabansu na ‘yan sandan Idris ya kuma bayar da umurnin a tsaurara dukkanin tsaro a lunguna da saqon cikin Abuja gami da sanya shingayen bincike ta kowane yanki na cikin babban birnin tarayya Abuja, domin tabbatar da bincikar kowace mota haxe da tabbatar da dawo da sandar ikon majalisar da kuma taso qeyyar

Badaqalar sace sandar majalisa

waxanda suka sace sandar, idan halin hakan ya bayar (sai dai hakan bai samu ba har lokacin kammala rahotan nan). Ya ci gaba da cewar sashin rundunar na musamman masu aikin bibiya, sun himmatu ka’in-da-na’in wajen tabbatar da tsaurara tsaro da kuma binciken dukkanin abun da suka gani ko suke tsammanin sandar tana wajen domin a samu nasarar qwatota daga hanun waxanda suka yi awon gaba da ita.

Ya bayyana cewar sandar sun samo ta ne a gefen hanya gabanin qarasawa zuwa ga kofar mashigar Abuja, inda wasu masu wucewa suka hangota haxe da sanar wa rundunar ‘yan sandan. Ya kuma shaida cewar har zuwa yanzu bincikensu kan wannan lamarin na ci gaba da gudanuwa domin tabbatar da cewar an sanqamo masu laifi kan lamarin domin kai su ga zuwa gaban shari’a domin fuskantar laifukansu.

Mai magana da yawun rundunar ya nuna matuqar godiyar rundunar ‘yan sandan ga jama’a da suka yi ta taimaka masu da bayanai da kuma sanar musu da dukkanin motsin da suka gano domin a samu nasarar. Ya nuna gayar farin cikinsu ga masu motocin haya da na hawa da suke Abuja a bisa taimako da haxin kai da suka bayar wajen binciken wannan sandar wacce har aka kai ga samun nasarar dawo da ita hanu mai kyau.

Ya bayyana cewar har a gobe dai aikin ‘yan sanda ne tabbatar da kare lafiya da dukiyar ‘yan qasa, yana mai bayyana cewar za su kuma ci gaba da qara himma a wannan fannin domin ci gaba da bayar da tsaro a gasar nan. Wakilinmu ya labarto cewar sai dai rundunar ta ‘yan sanda har zuwa yanzu ba su sanar da cewar sun kama ko da mutum guda daga cikin waxanda ake zargi da sace sandar ba, ba a kuma bayyana wa duniya dalilinsu na wannan satar ba.

Za A Cigaba Da Xaukar Malaman Firamare A Kaduna –Kwamishinan Ilimi Daga Ibrahim Ibrahim, Kaduna Kwamishinan Ilimi, Kimiyya da Fasaha na Jihar Kaduna, Alhaji Jafaru Sani, ya bayyana cewa, Gwamnatin Jihar Kaduna nan ba da jimawa ba za ta ci gaba da xaukar malaman firamare a jihar. Kwamishinan ya bayyana haka ne a yayin da yake zantawa da manema labarai a ofishinsa dake Kaduna. Jafaru Sani ya ce, yanzu haka Hukumar Ilimi ta Bai xaya ta kammala duk aikin xaukar malaman firamare kashi na farko, wanda bayan jarrabawa da ganawa, da tantancewa, an samu nasarar xaukar malamai 11,395 cikin malamai 25,000 da za a xauka. Yanzu haka waxannan malaman an tura su qananan hukumomi da makarantun da za su koyar”. Sannan game da ci gaba da xaukar sauran cikon malaman, kwamishinan ya bayyana cewa, nan ba da jimawa ba za su ci gaba da wannan aiki na xaukar malaman firamare har sai an samu qwararrun malamai 25,000 da Gwamnatin Jihar ke son ta xauka. Ya ci gaba da bayyana cewa, “Gwamnatin Jihar Kaduna za ta xauki qwararrun malamai guda 25,000 don haka yanzu bayan an tace, an tankaxe mun samu nasarar xaukar malamai 11,395, kuma duk an tura su inda za su yi aiki. Bayan haka, muna da

takardun masu neman aikin koyarwa aqalla 19,000 a qasa wanda nan ba da jimawa ba za mu yi masu jarrabawa don cike gurbin 25,000 xin da muke son xauka. Sannan za a ci gaba da xaukar malaman firamare har sai ya zamana kowane malami yana karantar da xaliban da ba su wuce 40 a aji ba” Kwamishinan ya qara da bayyana

cewa, “Kamar yadda aka sani a wannan xaukar malaman, mun karvi takardun neman aiki na sama da mutum 40,000, muka tantance muka rairaye muka fitar da sama da mutum 25,000 da suka zauna jarrabawar. Sannan kuma sama da mutum 15,000 suka sami nasarar cin jarrabawar. Bayan nan kuma wurin ganawa da

qara tantancewa muka sami malamai 11,395 wadda yanzu haka an tura su makarantun da za su koyar”. Haka kuma game da sabon tsarin albashi, kwamishinan ya ce, “Mun yi qudurin fara biyan albashi da sabon tsarin albashi a watan da ya gabata, amma saboda rashin kammala aikin xaukar sababbin malaman nan, shi ya

sa muka bari sai an kammala duka . Yanzu haka muna sa ran duk ranar da za a fara biyan sababbin malaman firamaren da aka xauka, za a fara da sabon tsarin albashi kamar yadda aka yi alqawari, kuma wannan zai haxa har da tsofaffin malamanmu”. A cewar Kwamishinan Ilimi na Jihar kaduna, Alhaji Jafaru Sani.

Kafa Asusun Tallafa Wa Xalibai Xaya Ne Daga Manyan Ayyukanmu –Sanata Kani Daga Abba Ibrahim Wada Gwale Shugaban qungiyar xalibai ta jami’ar Bayero da ke kano, Muhammad Sanusi Qani, ya bayyana cewa kafa asusun tallafa wa xalibai marasa qarfi da gwamnatinsa ta yi yana xaya daga cikin ayyukan da ta ke alfahari da su. Shugaban ya bayyana haka ne a wata hira da ya yi da manema labarai a ofishinsa da ke sabuwar jami’ar inda ya ce akwai tsare-tsare da gwamnatinsa ta zo da su kuma a hankali za su cigaba da aiwatar da su domin cigaban xaliban makarantar. Ya ci gaba da cewa gwamnatinsa tana iya qoqarinta wajen tabbatar da ganin cewa ta sauke nauyin da aka xora mata da kuma cika alqawuran da suka xauka a yayin yaqin neman zave. Ya qara da cewa duk da cewa

akwai matsaloli da gwamnatinsa take fuskanta amma hakan baisa sunyi qasa a gwuiwa ba wajen tabbatar da ganin komai yana tafiya yadda ya kamata a gwamnatin. Qani, yace wasu daga cikin ayyukan da gwamnatinsa takeyi sanatoci da masu ruwa da tsaki acikin gwamnatinne suke yi da kuxaxensu domin dai a tabbatar an sauke nauyin da yake kansu sannan kuma ya yi kira ga masu yiwa gwamnatinsa zagon qasa da su yi adawa irin wadda ya kamata batare da suna yin abinda zai dinga tauyewa xalibai haqqunansu ba. “Inason in ja hankalin xalibai cewa akwai wasu mutane da suke musu bita da qulli a gwamnatinsu domin su samu matsala saboda haka bazasu saki jika ba kuma zasu cigaba da ayyuka domin cigaban xalibai”. In

ji Sanata Qani. A qarshe ya bayyana wasu daga cikin muhimman ayyukan da gwamnatinsa tasamu nasara akai sun haxa da roqon hukumar makaranta akan kada ta qarawa xalibai kuxin makaranta sannan kuma an samu ragin kuxin makarantar a wasu tsangayun na jami’ar. Yace har ila yau gwamnatinsa tayi qoqarin samar da injin transifoma ga mutanen unguwar xan bare sakamakon akwai xalibai dayawa da suke zaune a unguwar sannan kuma sunyi qoqarin gyara kujerun karatu da suka lalace a xakunan karatu na jami’ar. Sannan kuma gwamnatinsa ta yi qoqarin bijiro da wani tsari na tallafawa xalibai yan asalin jihar nan inda xalibai 200 ne sukaji gajiyar

shirin a wannan shekarar sannan kuma shekara mai zuwa ma adadin xaliban zai iya qaruwa. Ya kuma godewa hukumar jami’ar Bayero bias goyon baya da suke bawa gwamnatinsa sannan ya jinjinawa xalibai suma bisa qoqarinsu na ganin komai yatafi yadda aka tsara.

Sanata Kani


LABARAI 27

A Yau Juma’a 20 Ga Afrilu, 2018 (26 Ga Sha’aban, 1439)

2019: Buhari Ya Cancanci Sake Tsaya Wa Takara –Sani Fema Daga Muhammad Sani Chinade, Damaturu

Tsohon shugaban hukumar wasanni na jihar Yobe, Alhaji Muhammad Sani Fema, ya bayyana cewar, Shugaban Qasa Muhammadu Buhari ya cancanta da sake tsayawa takara a karo na biyu, don cigaba da gyara irin varnar da gwamnatin PDP ta yi a tsawon shekaru 16 da suka yi suna mulkar qasar nan. Alhaji Sani Fema ya bayyana hakan ne a tattaunawarsa da wakilinmu a garin Damaturu bisa ga bayyana sake tsayawarsa takara a zaven da ke tafe na 2019 da shugaban qasar ya sanar a kwanakin baya wanda hakan ya kawo qarshen cece-kucen da ake ta yi dangane da yiwuwa ko rashin yiwuwar sake tsayawar shugaban. Kamar yadda ya ce tabbatacce ne cewar, Shugaba Buhari ya yi matuqar taka rawar gani a fannoni da dama musamman bisa alqawuran da ya xauka ya yin yaqin neman zave a 2015 kan abin

EB ZB TIBĂŤ LBXP RBSTIFO take-taken masu ta da qayar bayan Boko Haram da magance mummunar xabi’ar nan ta cin hanci da rashawa da a baya ke qoqarin laqume qasar nan, da kuma havaka tattalin arziqin qasar nan. Alhaji Sani Fema ya ci gaba da cewa duk wanda zai auna irin ayyukan da wannan gwamnati ta Muhammadu Buhari ta aiwatar a ‘yan shekaru 3 kacal da ta yi akan mulki musamman kan abin EB ZB TIBĂŤ IBSLPLJO UTBSP da tattalin arziki, da yaqi da almundahana na kwasar dukiyoyin jama’a, lallai za a ga cewar ya zarta mulkin PDP na shekaru 16 inganci. Ya qara da cewa in aka xora wannan gwamnati a mizani na haqiqa sai a ga cewa, gwamnatin a qarqashin shugabancin Muhammadu Buhari ta cimma muhimman nasarori musamman wajen ayyukan raya qasa da suka haxa da gina hanyoyi, samar da aikin yi ga matasa, da inganta tattalin arziki, da qara inganta harkokin ilimi, samar da

tsaro ba tare tsumbure da NBLBNBOUBOTV CB ÍZF EB kashi 75 cikin 100. Don haka ya kirayi dukanin al’ummomin

Jihar Yobe da na Jihohin Arewa maso gabas da na dukanin qasa baki xaya da su goya baya ga wannan mataki na shugaban qasa

na sake tsayawa takara a karo na biyu don ci gaba da qudirinsa na ceto qasar nan da al’ummominta daga halin ni ‘ya su.

•Sani Fema

Gwamnatin Yobe Ta Tura An Rantsar Da Sabbin Alqalan Xalibai 1,400 Karatu Shari’ar Musulunci A Bauchi Waje –Gwamna Gaidam Abubakar na qoqarin samar xaukaka qara ta shari’ar Daga Khalid Idris Doya, Bauchi

Daga Muhammad Sani Chinade, Damaturu

ce a yanzu haka gwamnatin Jihar Yobe ta xauki Gwamnan jihar Yobe, Alhaji xawainiyar xaliban Jihar Ibrahim Gaidam, ya bayyana kusan kimanin 1400 ya zuwa cewar, gwamnatin jihar a qasashen qetare don karo yanzu haka ta tura kimanin ilimi, ciki har da qasar Sudan xaliban jihar 1,400 ya zuwa cikinsu har da dalibai mata manyan makaratun qaro kimanin 80 da ke karatu a ilimi a wasu qasashen qetare. Jami’ar Ahfad. Tun farko da Gwamnan ya bayyana ya ke jawabi Dr. El-Bashir, hakan ne ya yin da ya ke wadda tsohon Janar ne na karvar baquncin mataimakin rundunar sojan qasar Sudan shugaban jami’ar kula da ne, ya ce jami’arsu ta AlLJXPO MBÍZB LJNJZZB EB Madain, a shirye ta ke da ta fasaha ta Al-Madain Abdullah ba da dama ga xaliban Jihar Hassan El-Bashir da ke qasar Yobe don samun ilimi mai Sudan, da ya kawo ziyara a inganci kamar yadda ake gidan gwamnatin Jihar dake bukata, don mayar da Jihar Yobe wacce ke da likitoci garin Damaturu. Ya qara da cewar Jihar Yobe masun yawan gaske a faxin za ta haxa gwiwa da Jami’ar qasar nan. Ya qara da cewa, Al-Madain, don ganin cewar xaliban jihar da yawa sun dangantakar da ke tsakanin amfana musamman kan Nijeriya da qasarmu ta vangaren samun horo na Sudan dangantaka ce mai aikin likitanci, da sanin matuqar armashi tsawon magunguna da horo a kan lokaci musamman kan abin darasin injiniya, da zaiyana EB ZB TIBÍ UBUUBMJO BS[JRJ EB siyasa, da al’adu da ilimi da da makamantansu. Kamar yadda gwamnan ya sauransu.

Hukumar Kotun shari’ar Musulunci da ke Bauchi ta rantsar da sabbin Alqalan manyan kotun shari’ar Musulunci a jihar, cikin makon nan. Hakan na daga cikin yunqurin hukumomin da abin ya shafa ne na tabbatar da yin shari’a kan lokaci a faxin jihar ta Bauchi, da kuma rage yawan cinkoson shari’u. Da yake jawabinsa jim kaxan bayan rantsuwar kama aikin sabbin Alqalan, Alqalin Alqalai na jihar Bauchi Xahiru Abubakar Ningi ya buqaci sabbin Alqalan da suka kasance masu gaskiya, da riqon amana, gami da yin adalci a lokacin da suke bakin ayyukansu na shari’a a kowani lokaci. Xahiru Abubakar Ningi ya jinjina wa gwamnatin jihar Bauchi, a qarqashin shugabancin Lauya Muhammad Abdullahi

da muhallan da suka dace wa vangaren shari’a. Alqalin Alqalai na jihar ta Bauchi, ya kuma yi amfani da wannan damar wajen yin kira ga gwamnatin jihar ta Bauchi da ta samar da gidaje ga masu shari’a guda uku da aka rantsar da su bisa bakin aiki kimanin shekaru uku da suka gabata. Da take nata jawabin, babbar mai Shari’a ta jihar Bauchi, Hajiya Rabi Talatu Umar, ta taya sabbin Alqalan murna a bisa wannan ci gaban da suka samu, sai kuma ya yi kira a garesu da su zage dantse wajen gudanar da ayyukansu bisa doka da kuma bin qa’idar da BJLJOTV ZB TIJNÍYB Babban Alqalin jihar, wacce ta samu wakilcin Mai shari’a Aliyu Umar, ta jaddada aniyarta na sanya qa’idojin aiki a xaukacin kotunan da suke jihar ta Bauchi. A tsokacinsa, babban Magatakardar kotun

Musulunci, Barista Sa’ad Muhammad Sambuwal ya ce, naxin sabbin Alqalan na daga cikin qoqarin da ake yi na samar da qarin ma’aikata a kotun qoli inda a bayabayan nan ake samun Alqali guda ke kula da kotuna biyu, wanda kuma hakan ke sanya ayyuka ke masa yawa. LEADERSHIP A YAU, JUMA’A ta naqalto mana cewar waxanda aka rantsar a matsayin sabbin Alqalan kotun Landiran shari’ar Musulunci ta Bauchi su ne Sani Musa Azare, da kuma Minka’ilu Sabo Ningi su ne sabbin alqalai da aka yi masu rantsuwar kama aiki. Sabbin Alqalan sun nuna jinjinarsu da ba su wannan damar haxe da shan alwashin bai wa marar xa kunya ta fuskantar yin dukkanin mai yiyuwa wajen tabbatar da kai sha’anin shari’a mataki na gaba, ta fuskar yin ayyukan da suka dace bisa gaskiya da riqon amana.


28

A Yau Juma’a 20 Ga April, 2018 (3 Ga Sha’aban, 1439)

WASIQU

08034980391 08069824895 leadershipayaujumaa@gmail.com

Duk abin da aka bayyana ba ra’ayin LEADERSHIP A YAU ba ne, ra’ayin waxanda suka aiko da saqonnin ne.

‘Tsakanin ‘Yan Shi’a Da Gwamnati, Ina Gizo Ke Saqa?

Assalamu alaikum, LEADERSHIP A YAU JUMA’A. Haqiqa mun yi farin ciki da sake ba mu dama wurin bayyana abubuwan da suke mana qaiqayi a rai tare da isar da saqon da muke son isarwa ga shugabanni da sauran al’ummar qasa. Muna muku addu’ar Allah ya qara muku hikima da basirar aiki da kuma bunqasar wannan jarida mai farin jinni baki xaya. Ni fa har yanzu a Nijeriya ba abin da yake kulle mun kai, ya hana ni fashin baqi kamar lamarin gwamnati da ‘Yan Shi’a, shi ya sa kullum tambaya nake yi me ya sa ake hallaka ‘yan Shi’a ne? 1- Idan saboda tawaye ne ga ‘yan qungiyar IPOB, Nnamdi Kanu bayan ya gama tsine wa Nijeriya da ‘yan Nijeriya, ya jawo har rundunar Sojan Nijeriya aka sauke masu, amma an ba da belin shi. Bayan nan ya karya dokar belin ya tsere amma har yanzu an kasa kamo shi a dawo da shi, duk da muna da ‘bilateral agreement’ na ‘extradition’ da Ingila. 2- In zangazanga ne a qasar nan an yi na ‘fuel subsidy’, shugaban qasa bashi da hujjar yaqi da zangazanga, duba da zangazangar zaven shi da aka ce an murde a 2003,2007,2011. Ga na bring back our girls. 3- Idan zagin Buhari ne ga wasu can ma sun bi shugaban qasa da placards a Ingila suna ta zagin shi gaban idon shi. Kuma kullum sai zagin shi ake yi a TV, Radio da kuma Facebook . idan ya ji haushin zagin me zai hana shi kaisu qara kotu?. 4- Abun mamaki shi ne wasu sai su ce saboda suna zagin Sahabbai, to ina ruwan ‘constitution din Nijeriya da sahabin Annabi. Wasu na tsammani “the MBCPS PG PVS IFSPFT GBTUw EJO BOB OVĂŤO sahabbai ne. To bari kuji a constitution din Nijeriya Sardauna da Azikwe da 5BGBXB #BMFXB TVOĂŤ TBIBCCBJ EBSBKB Harma ka cewa xan Sandan Nijeriya yana kare sahabbai ma wauta ce kawai. Rashin amsar waxannan tambayoyi suka sa nake da tabbas cewa zalumta ‘yan Shi’a ake yi a qasar nan. Saqo daga Muhammad Idris (Babanne), Abuja. 07065279510 Kira Ga Masu Neman Takarar Shugabancin Nijeriya A 2019 Assalamu alaikum, LEADERSHIP A YAU JUMA’A, ina so ku bani dama na faxi damuwata akan ‘yan siyasarmu, masu neman takarar qujerar shugabancin Nijeriya a zave mai zuwa na 2019. Da farko dai ya kamata su sani

zamani da yanayi na duniya ya canja an wuce qarnin da wasu tsuraru za su ci gaba da kwashe arzikin qasar mu suna kaiwa Turai suna azurta kansu da AZB ZBOTV .V NVO TBOJ NBĂŤ BLBTBSJO waxanda shugaban kasa ke tare da su da sanatoci da gwamnoni ba kaunarsa suke ba. Asali ma suke kawo vatanci da daqile duk wani abu da zai kawo ci gaban a kasa don sanya wa talaka qiyayyar Buhari a cikin zuciyarsu. Sun manta cewa Allah ne ke bada mulki. Kuma mun yi imani Allah zai qara baiwa Baba Buhari mulki da izinin Allah.

Saqo daga Uwaisu Buhari Imam, Sokoto. 07064756693

Ta ya Za a ce Artabu? Tsakanin Mabiya Aqidar Shi’a Da Jami’an Tsaro Salam, Editan LEADERSHIP A YAU JUMA’A, ina so ka bani dama na bayyana abin da ya ke ci min tuwo a qwarya. Abun dubawa ne qwarai yadda aka ce an yi artabu tsakanin mabiya aqidar Shi’a da Jami’an tsaro. Maganar gaskiya shi ne yana da kyau masu xauko rahoto da masu buga shi Kuma zan yi amfani da wannan su kasance masu xaukar gaskiya tare da dama na baiwa mai girma Sanata Rabiu buga gaskiya ba tare da nuna banbanci Musa Kwankwaso shawara da ya qara aqidan yare ,addini ko kuma launi ba. haquri, domin duk xan halal bai manta Na xan yi wannan tsokaci ne bisa alkairi. Ya jajirce ya tsaya a jam’iyyar abun da ya faru tsakanin mabiya akidar sa ta APC, wanda hakan zai zame masa shi’a da kuma jami’an tsaro a babban alkairi in sha Allah. birnin tarayya abuja. Kamar yadda da yawa daga cikin Mulki lamari ne na Allah saboda kafafen yaxa labarai kan cewa anyi duk a ‘yan takarar ba mai nagartar artabu tsakanin mabiya akidar shi’a Kwankwaso a ciki waxanda suke neman da jami’an tsaro, maganar gaskiya ba shugaban qasa. Sauran duk ‘yan amshin haka rahoton yake ba domin kuwa TIBUB OF 4BCPEB ĂŤUPXBS TB ZB LBSB babu yadda za’a ce anyi artabu tsakanin da Buhari zai bata siyasar sa kamar ta mutumin dake rike da kwalli da kuma Atiku Abubakar. Ya qara haquri saboda jami’an tsaro dake rike da bindiga da duk mai hankali da bincike da nazari ya motoci, wannan sam bazai yuwu ba. san akwai abin da Allah ya shirya a kan Maganar gaskiya shi ne ba artabu aka #VIBSJ UVO EBHB SBTIJO MBĂŤZBSTB EB DJO yi ba, an samu rashin fahinta ne kuma mulkinsa. daga baya jami’an tsaro suka yi amfani Saboda haka duk wanda zai yi jayayya EB RBSĂŤOTV XBKBO UBSXBUTB NBCJZB UBNLBS EB "MMBI [BJ ZJ %VL XBOJ UTBĂŤ akidar shi’a lokacin da suke xauke da da kashe jarirai da surkulle, wallahi ba kwallayen nuna rashin goyon bayansu [BJ IBOB #VIBSJ NVMLJ CB TBJ EBJ LBSĂŤO ga gwamnati bisa cigaba da take yi na Allah kaxai zai hana shi wucewa. Amma tsare malaminsu kimanin shekaru uku da izinin Allah sai Baba Buhari ya yi ba bisa qa’ida ba. takwas.

Jan hankali, a matsayina na mai aikin yaxa labarai da rahotanni, nauyi ya rataya akai na, na faxin gaskiya akan kowa ba tare da nuna banbanci ba kamar yadda aikin jaridanci ya tanadar. Haka kuma masani a aikin jaridanci na duniya xan qasar Indiya Farfesa Sharma ya qara tabbatar da hakan DJLJO MJUUBĂŤOTB NBJ TVOB FEJUPSJBM BOE reporting in journalism) a turance, don haka banyi wannan rubutu domin goyon baya ko kuma kuntatawa wani, a’a tsabar gaskiya ce data wajaba na bayyana domin saukar da nauyin dana xaukar ma kaina. Saqo daga Auwal M Kura, Kano. Shawara Ga Matasa Assalamu Alaikum LEADERSHIP A YAU Juma’a, ina so ku bani daman a bayyana ra’ayina ga mutanen Nijeriya musamman matasa. Na farko, ina kira ga matasa dole ne ku tashi tsaye, ku cire tsoro da SBHXBODJ LV ĂŤUP B GBGBUB EB LV B DJLJO duniyar neman ‘yanci da sanin kai. Matasa lokaci yayi da ‘yan siyasa za su dena amfani da mu,wajen cimma burin TV EB NBOVGPĂŤOTV XBOEB CB DJHBCBO al’umma ba,kuma bana kishin kasa ba. Matasa lokaci yayi da zamu nunawa ‘yan siyasa cewa kan mu a haxe yake, su dena bamu makamai da kayan maye muna halakar da junanmu saboda cikar burinsu da kuma kariya ga jam’iyyunsu. .BUBTB NV ĂŤUP NV HBZBXB AZBO TJZBTB mun dena siyasar duhun kai,mun dena siyasar kuxi ko jam’iyya. Saqo daga Isma’il Yusuf, Kagarko. 08168499372


A Yau Juma’a 20 Ga Afrilu, 2018 (3 Ga Sha’aban, 1439)

TALLA 29

Gaba dai! Gaba dai “Super Eagles�

Bankin Zenith na taya ‘yan qwallon Nijeriya “Super Eaglesâ€?, murna sakamakon nasarar da suka samu ta kai wa gasar Cin ,PĂŤO %VOJZB XBOEB [B B HVEBOBS B RBTBS 3BTIB


A Yau Juma'a 21.4.2018

Wasanni

30

Tare da Abba Ibrahim Wada -FBEFSTIJQ "ZBV!ZBIPP DPN

Pogba Ya Raina Mourinho, In Ji Paul Scholes Daga Abba Ibrahim Wada Gwale

Ina Dab Da Dawowa Daga Jinya - Neymar 9BO XBTBO HBCB OB RVOHJZBS RXBMMPO RBGB UB 14( YBO RBTBS #SB[JM ZB CBZZBOB DFXB ZBOB LBO IBOZBSTB UB EBXPXB EBHB KJOZBS EB ZBLFZJ CBZBO BOZJ NBTB UJZBUB B RBGBSTB B XBUBO 'BCSBJSVO EBZB HBCBUB TBLBNBLPO SBVOJO EBZBKJ B RBGBSTB /FZNBS ZB CBZZBOB IBLB OF B XBUB IJSB EB ZBZJ EB NBOFNB MBCBSBJ B #SB[JM JOEB ZBDF LPNBJ ZBOB UBรถZB ZBEEB ZBLBNBUB LVNB OBO CBEB KJNBXB CB [BJ GBSB YBVLBS IPSP /FZNBS XBOEB ZBรถ LPXBOOF YBO

XBTB UTBEB B EVOJZB ZB CBZZBOB DFXB CB[BJ TBLF CVHBXB RVOHJZBSTB UB 14( XBTB CB TBCPEB MPLBDJO EB [BJ EBXP BO LBNNBMB HBTBS RBTBS 'BSBOTB TBJ EBJ ZBDF ZBOB HBOJO [BJ EBXP EPNJO TIJSJO HBTBS DJO LPรถO EVOJZB :BDJ HBCB EB DFXB TIFLBSB IVYV LFOBO ZBOB KJSBO XBOOBO MPLBDJO ZB[P EPNJO HBOJO ZB UBJNBLBXB RBTBSTB XBKFO MBTIF HBTBS DJO LPรถO EVOJZB XBOEB [B BZJ B RBTBS 3BTIB :B RBSB EB DFXB BO EVCB DJXPO OBTB SBOBS HB XBOOB XBUBO

LVNB MJLJUBO ZB TIBJEB NBTB DFXB LPNBJ ZBOB UBรถZB ZBEEB ZBLBNBUB TBCPEB IBLB OBO EB NBLPOOJ IVYV [BJ NVSNVSF LVNB ZBGBSB YBVLBS IPSP EPNJO UVOLBSBS RBMVCBMFO EBLF HBCBOTB OB HBOJO TVO MBTIF HBTBS DJO LPรถO EVOJZB " RBSTIF LVNB ZB CBZZBOB GBSJO DJLJOTB HB RVOHJZBS TB UB 14( CBZBO EB RVOHJZBS UB MBTIF LPรถO SVLVOJ SVLVOJ na qasar Faransa a satin daya gabata JOEB ZBDF ZBOB OBO ZBOB NVSNVSFXB LVNB [BJ EBXP EB RBSรถOTB

Zaratan City Sun Mamaye Gasar Firimiyar Bana Wata qungiyar qwarrru da ke kula da โ yan wasan da suka nuna bajinta a gasar รถSJNJZB RBTBS JOHJMB B LPXBDDF TIFLBSB UB รถUBS EB TVOBZFO AZBO XBTB XBYBOEB B DJLJOTV OF [B UB รถUBS EB NBรถ IB[BRB CBOB B HBTBS UB 'JSJNJZB %BHB DJLJO AZBO XBTBO XBEBOEB EBHB DJLJ TVO รถUP OF EBHB .BODIFTUFS DJUZ NBJ SJRF EB LBNCV DJLJO AZBO XBTBO EBJ BLXBJ ,ZMF 8BMLFS EB /JDPMBT 0UBNFOEJ EB %BWJE 4JMWB EB ,FWJO %F

#SVZOF EB LVNB 4FSHJP "HVFSP *UB NB EBJ RVOHJZBS RXBMMPO RBGB UB 5PUUFOIBN OB EB AZBO XBTB EB BLB TBOZB DJLJO KFSJO AZBO XBTBO NBรถZB IB[BLB EB TVLB IBEBS EB )BSSZ ,BOF EB %FMMF "MMJ EB LVNB $SJTUJOF &SJDLTPO 4BJ LVNB NBJ UTBSPO SBHBS RVOHJZBS RXBMMPO RBGB UB .BODIFTUFS 6OJUFE %BWJE EF (FB XBOEB TIFLBSB CJZBS LFOBO B KFSF ZBOB TIJHB DJLJO XBOOBO KBEBXBMJ

)BLB [BMJLB BLXBJ YBO XBTBO HBCB OB -JWFSQPPM .PIBNFE 4BMBI YBO XBTBO EB ZB LBGB UBSJIJ UB IBOZBS [VSB RXBMMBZF DJLJO LBLB HVEB XBOEB LVNB UVOJ BLB TBOZB TVOBOTIJ DJLJO KFSJO AZBO XBTBO EB [B B UBOUBODF NBรถ IB[BRB DJLJOTV B CBOB *UB LVXB $IFMTFB OB EB YBO XBTB HVEB OF YBZB TIJHB DJLJO KFSJO XBUP .BSDPT "MPOTP XBOEB BLB EBLBUBS B KJZB TBLBNBLPO OVOB IBMJO SBTIJO YB B B XBTBO RVOHJZBS OB SBOBS "TBCBS

5TPIPO YBO XBTBO RVOHJZBS RXBMMPO RBGB UB .BODIFTUFS 6OJUFE 1BVM 4DIPMFT ZB CBZZBOB DFXB YBO XBTBO RVOHJZBS XBOEB ZBรถ LPXB UTBEB 1BVM 4DIPMFT ZB SBJOB .PVSJOIP TBLBNBLPO JSJO RXBMMPO EBZB CVHB B XBTBO RVOHJZBS EB 8FTUCSPN 4DIPMFT ZB CBZZBOB IBLBOF B IJSBSTB EB XBOJ HJEBO UBMBCJKJO JOEB ZBDF JSJO ZBEEB ZB CVHB RXBMMP B XBTBO EB TVLB TIB LBTIJ IBS HJEB B IBOOVO 8FTUCSPN ZB SBJOBXB .PVSJOIP IBOLBMJ TBCPEB XBTBOTB LBXBJ ZB CVHB B XBTBO :BDJ HBCB EB DFXB CBJ CVHB XBOJ BCVO LJSLJ CB B XBTBO LBXBJ UTBMMF UTBMMFOTB ZBZJ BDJLJO รถMJO TBCPEB IBLB .PVSJOIP ZBZJ EBJ EBJ EBZB DJSFTIJ B NJOUJ OB EB GBSB XBTBO EPNJO ZB HBOF DFXB CBZB RPRBSJ ZBEEB ZBLBNBUB :B RBSB EB DFXB CB LBXBJ 1PHCB CBOF CBZB RPRBSJ TIJNB YBO XBTBO EB RVOHJZBS UB TJZP LVNB ZBรถ LPXBOOF YBO XBTB YBVLBS BMCBTIJ "MFYJT 4BODIFT CBZB RPRBSJ LVNB ZBLBNBUB ZBGBSB OVOBXB EVOJZB DFXB TIJOF 4BODIFT YJO EB BLB HBOJ B #BSDFMPOB UB "STFOBM " RBSTIF ZBDF 1PHCB EB 4BODIFT CBCV LBNBSTV B RVOHJZBS TBCPEB IBLB ZBLBNBUB TV GBSB OVOBXB EVOJZB DFXB [BTV JZB SJRF SBHBNBS .BODIFTUFS 6OJUFE OBO EB XBTV ZBO TIFLBSV JEBO LVNB CB IBLB CB UBCCBT TJZBOTV CBTIJ EB BNGBOJ .BODIFTUFS 6OJUFE EBJ JUBDF B NBUTBZJ OB CJZV BLBO UFCVSJO รถSJNJZB TBOOBO LVNB [BUB CVHB XBTBO LVTB EBOB RBSTIF EB RVOHJZBS 5PUUFOIBN B SBOBS "TBCBS B HBTBS DJO LPรถO RBMVCBMF OB '"


A Yau Juma’a 20 Ga April, 2018 (3 Ga Sha’aban, 1439)

WASANNI 31

Wariyar Launin Fata: FIFA Za Ta Hukunta Rasha Matuqar… Daga: Abba Ibrahim Wada Gwale

da suka yi wa wasu ‘yan wasa kalaman vatanci na kiransu Birai a Rasha Hukumar qwallon qafa ta duniya, FIFA ta bayyana Mai magana da yawun Hukumar FIFA ya ce Huxaukar matakin ladabtarwa ga wasu ‘yan kallo kumar ta xauki matakin ladaftar da mai xaukar baquncin gasar cin Kofin qwallon qafa ta Duniya wato qasar Rasha akan wasu kalaman vatanci na kiran wasu ‘yan wasa dasunan Birai da aka ji wasu ‘yankallo na yi a lokacin da ake gudanar da wasan sada zumunci ta qasa da qasa tsakanin qasar ta Rasha da Faransa. An ce dai masu kiran Biran na shaguve ne ga dan wasar tsakiya na Manchester United Paul Pogba da na Barcelona Ousmane Dembele ne a lokacin da aka ji su suna kiran Birai, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na kasar Faransa AFP ya sanar. To saidai ita kanta hukumar qwallon qafa ta Rasha ta ce a shirye take ta bada haxin kai dangane da wannan batun na cin zarafi da aka ji wasu ‘yan kallo suna yi wa ‘yan wasa, har ma ita hukumar qwallon qafar ta Rasha na cewar sun kafa nasu kwamitin bincike akan wannan zargin. Qasar Rasha dai tayi suna wajen nuna wariyar launin fata musamman gay an qwallon qafa Daga Abba Ibrahim Wada Gwale baqaqen fata da suke buga wasa a qasar har ila yau kuma a qasar za’a buga gasar cin kofin duRahotanni daga qasar sipaniya sun bayyana niya na bana. cewa qungiyar qwallon qafa ta Real Madrid tanason yin musanye da Liverpool domin ta xauki Muhammad Salah yayin da kuma Benzema yakoma Liverpool xin da buga wasa. Shugaban gudanarwar qungiyar ta Real Madrid ne dai yakeson wannan ciniki saboda yana tunanin idan akayi haka zai samu sauqin da Bayern Munich da Real Madrid kasance a Amurka ne, a yayin da xaukar Salah tunda yasan duk da haka sai ya Daga Abba Ibrahim Wada Gwale da Roma da Liverpool kazalika da sauran aka saka su a qasashen cikawa Liverpool kuxi akan Salah. Benzema dai yana shan suka daga wajen Manchester City da Manchester Singapore da Switherland da A Ingila an bayyana manyan United ne. Austria da Poland da Sweden da magoya bayan qungiyar sakamakon rashin qungiyoyin wasanni 6 na Ingila da qoqarinsa qungiyar a wannan shekarar wanda Gasar wadda aka shirya buga Italy da Spain. suka kai ga wasa kusa dana qarshe ta tsakanin qungiyoyin wasa 18 Tuni dai shirye-shirye sunyi nisa yasa har yanzu qwallaye biyar ya zura a raga a na daga cikin kungiyoyin wasan a karawa 27 a kuma kasa da Sati na ganin gasar ta samu karvuwa laliga hakan yasa Real Madrid takeson rabuwa da ake kira gaggan qungiyoyin daya bayan kammala gasar cin a wajen masoya qwallon qafa a da xan wasan domin kawo Salah wanda wasa da kuma ake sa ran za su Kofin qwallon qafa ta Duniya a faxin duniya inda aka shirya idan tauraruwarsa take haskawa yanzu a duniya. samu damar shiga gasar cin Kofin kasar Rasha, akasarin wasannin har gasar tayi armashi za’a dinga Ya zura qwallaye 40 a Liverpool kawo yanzu qasa da qasa na championship. kuma yafi kowanne xan wasa yawan zura da za’a buga a cikinta sun gudanarwa duk shekara. Kungiyoyin wasan dai sun haxa qwallo a raga a gasar firimiya ta qasar ingila sannan kuma ya taimakawa qasarsa taje gasar cin kofin duniya da za’ayi a qasar Rasha. Sai dai mai koyar da yan wasan Liverpool, Jurgen Klopp, xan qasar Jamus ya bayyana cewa xan wasa Salah bana siyarwa bane zakarun turai a ranar Laraba. gashi kuma yanzu akwai babban saboda haka duk qungiyar da takeson siyansa Daga Abba Ibrahim Wada Gwale Zidane ya bayyana hakane wasa a gabansu na wasan kusa sai dai tayi haquri. Liverpool da Real Madrid dai duka sun kai bayan da qungiyarsa ta buga 1-1 dana qarshe na cin kofin zakarun da qungiyar Athletico Bilbao har turai hakan yana nufin dole sai sun wasan kusa dana qarshe na cin kofin zakarun Mai koyar da yan wasan qungiyar gida a wasan laliga inda Cristiano tashi tsaye sun dage domin bawa turai inda Real Madrid zata fafata da Bayern qwallon qafa ta Real Madrid, Ronaldo ya farkewa qungiyar maraxa kunya. Munchen yayinda Liverpool zata kece raini da Zinedine Zidane ya bayyana cewa qwallon da aka zura mata a minti Yaci gaba da cewa abune mai AS.Roma ta qasar italiya. bai kamata qungiyar ta dogara da na 87 da wasan. wahala doke qungiyar Bayern xan wasa Cristiano Ronaldo ba Zidane yace kowanne xan wasa Munchen sai dai kuma qungiyarsa a wasansu na gaba da qungiyar a qungiyar zai iya zura qwallo a raga itace mai kare kambu saboda haka Bayern Munchen a wasan na ba kawai Ronaldo ba saboda haka akwai buqatar su nunawa duniya cewa sune Real Madrid ta hanyar doke Bayern xin domin zuwa wasan qarshe. Ya qara da cewa ya damu da rashin zura qwallo a raga da yan wasansa suke ciki amma kuma bai damu ba da rashin qoqarin Bale wanda ya shigo bayan an dawo daga hutun rabin lokaci. A warshe yace yanzu yazama dole su mayar da hankalinsu wajen ganin sun samu nasara a wasan gaba da Bayern Munchen domin gasar zakarun turai ita kaxai ce ta ragewa qungiyar a wannan kakar.

Madrid Na Son Musanyen Benzema Da Salah

Madrid, United, City Da Liverpool Za Su Kara A Wata Gasa

Ba Za Mu Dogara Da Ronaldo Ba A Wasanmu Da Bayern Munchen - Zidane


20.04.18

AyAU LEADERSHIP Don Allah Da Kishin Qasa

www.leadershipayau.com Leadership A Yau

JARIDAR HAUSA

LeadershipAyau

Juma’a 20 Ga Afrilu, 2018 (3 Ga Sha’aban, 1439)

MAI FITOWA KULLUM TA FARKO A NIJERIYA

Bugu na: 032

N150

WASANNI

Madrid Na Son Musanyen Benzema Da Salah > Shafi na 31

Kada A Ci Moriyar Ganga A Alqalami Mance Da Kwaure! (4)

Dr. Ibrahim Shehu Liman

(08023703718) ibrahimshehu781@yahoo.com

A makon jiya alqalaminmu ya ya-da zango ne a gavar da ke qalubale kan gudunmuwar da zaqaquran ‘yanwasa irin su Shu’aibu Maqarfi, Adamu Gumel, Muhammadu Ango Zariya, Yusufu Ladan, Qasimu Yero, Usman Baba Pategi, da makamantansu. A wancan karo mun yi hannunka-mai sanda kan su wane ne azsu iya tsarawa, su rubuta su kuma jagoranci aiwatar da nagartattun wasannin kwaikwayo. ko da kuwa akwai, tun da irin Allah ba ya qarewa, to sai an ja-xamara. Dalili kuwa, su a wancan lokaci ba sa yin waxannan hidimomi don a tattaro musu wasu maqudan kuxaxe, kuma babu tunanin shashanci. Ire-iren waxannan qwararru kan wasan kwaikwayo sun yi tarayya kan wasu halaye dangane da yadda suka doshi harkar rubuta wasannin. Kamar sauran takwarorinsu marubuta fannonin adabi daban-daban, za a iya la’akari da cewa wasu muhimman abubuwa sun yi tasiri a rubutunsu waxanda suka haxa da: • Kowannensu ya rungumi harshensa na asali ne wajen yn rubutunsa. • Zamanin da suka samu kansu a ciki, wato zamani ne da ba a daxe da bankwana da Turawan mulkin mallaka ba, inda ake qoqarin murmurewa da kuma neman mafita kan sababbin matsalolin da suka addabi al’umma. • Yanayin yadda al’ummar da suke ciki ke gudanar da nazari da sauran ayyuka da suka danganci ilimi da fasaha da basira. • Sanin abin da za a gina wasan a kan sa, wato maqasudin wasa, kamar kishin qasa, gyaran tarbiyya, shugabanci da makamantansu. • Yin rubutu bisa tsari, mai cike da basira da kuma ma’ana.

•Usman Baba Pategi

• Amfani da taurarin wasa wajen bayyana yadda ake shawokan matsalolin da aka samu kai a cikinsu. Daga cikin duka masu rubucerubucen adabi na Hausa da ake da su, marubucin wasan kwaikwayo ya zama kan gaba wajen bayyana yanayin rayuwar al’umma da kuma kawo sauyi ko gyara kan matsalolin da ke addabarta, saboda ta hanyar wasan ne kawai ake iya bayyana abubuwa qarara. Kasancewar waxannan gwarzaye da muka ambata a baya sun laqanci yanayin rayuwar al’ummominsu, sun yi amafani da take daban-daban da suka jivanci abubuwan da ke faruwa a tsakanin waxannan al’ummomi. Haka nan wasannin da waxannan gwanaye suka rubuta sun samu karvuwa ga masu nazari a ilmance da kuma sauran masu sha’awa. Dalili kenan ma da ya sa ake fassara ayyukansu, da juya su zuwa salon rubucerubuce da dama , da aiwatar da su a gidajen rediyo da talabijin da kuma faxaxa nazari a kansu.

•Qasimu Yero

Kodayake masanin adabin Hausan nan, Gusau, S.M (2008), na ganin harshen Hausa yana da yalwa da faxi ta yadda za a iya amfani da shi don gabatar da kowane irin nazari da ake son gabatarwa ko aiwatarwa idan dai an yi hovvasa kan haka; Haka kuma Hausa, harshe ne wanda yake karvar ci gaba ta hanyar saduwa da baqin al’adu, to amma da sake, don kuwa da adabin da kuma shi harshen ba sa yarda da duk abin da zai zama maigurvatasu. Da zaran an ga wani baqon abu da aka shigo da shi da zai yi barazana game da abin da aka amince da shi, to sai a yi watsi da shi. Wani fasihin Hausa, Abubakar Ladan Zariya ya matsa qaimi wajen qarfafa gwiwar ‘yan Afirka da suka haxa har da Hausawa da sauran al’ummomi kan su dage, su kuma kula da adabi, al’adu da kuma fasahohin da Allah ya albarkace su da su: “Mu tsaya mu riqe al’adunmu, Su akka qawata Afirkanmu,

Har ma wasu sui sha’awar namu, Shi ne darajarmu da haibarmu, Mai nuna muna da abin kanmu” A nan zamu xan tsahirta, a makon gobe idan Allah ya yarda zamu xora, mu qarqare waiwayen da muke yi kan mashahuran marubuta da shirya wasan kwaikwayo na Hausa. A huta lafiya.

Babba Da Jaka Sanata Omo-Agege ya jagoranci sace sandar majalisa - Labarai

Hala xan’uwan Orubebe ne?

Ana shiryawa da buga LEADERSHIP A Yau a kamfanin LEADERSHIP GROUP LIMITED, lamba 27, kan Titin Ibrahim Tahir, a Gundumar Utako, Abuja. Tarho: 08039216372 Fax: 09-2345360. P. O. Box 9514, Garki II, Abuja. Ofishin mu a Legas: 34/36 Titin Adegbola, Anifowose, daidai Oba Akran, Ikeja. Tarho: 01-8963459. E-mel:leadershipayaujumaa@gmail.com


Turn static files into dynamic content formats.

Create a flipbook
Issuu converts static files into: digital portfolios, online yearbooks, online catalogs, digital photo albums and more. Sign up and create your flipbook.